Jami’an Shirin Tallafa Wa Noman Auduga Na Kasar Sin Karo Na 4 Sun Isa Kasar BeninDaga CGTN HausaJami’an shirin tallafa wa noman auduga na kasar Sin karo na hudu a kasar Benin sun isa kasar a jiya Laraba domin fara aiki, a wani bangare na hadin gwiwar fannin aikin gona tsakanin Sin da kasar ta Benin dake yammacin Afirka.
Ana sa ran jami’an shirin su shida za su yi tattaki nan ba da dadewa ba daga Cotonou, babban birnin kasar, inda ake da tashar jiragen ruwa mafi girma ta kasar zuwa Parakou dake arewacin kasar, inda za su gudanar da ayyukan bunkasa noman auduga a kasar Benin, wadda ita ce kan gaba wajen noman auduga a Afirka.
A yayin zamansu a Parakou, wata muhimmiyar cibiyar noman auduga ta kasar Benin, kwararrun na kasar Sin za su taimakawa manoma wajen zabar iri mai inganci, da inganta fasahohin noma, da samar da kwarewar sarrafa injunan noma, da kuma horar da ma’aikatan kula da kayan aiki ‘yan kasar Benin.
Tun bayan kaddamar da shi a shekarar 2013, shirin tallafawa noman auduga na kasar Sin a kasar Benin ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta zamanantar da aikin gona na kasar. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post