ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gadar Oporoma a jihar Bayelsa ta Najeriya ta kara hada zukatan jama’ar Sin da Najeriya

by Sulaiman
2 months ago

Kwanan nan, an kammala gina babbar gadar Oporoma a jihar Bayelsa ta Najeriya kuma aka kaddamar da ita. Wannan gada mai tsawon mita 630 wadda kamfanin China Civil Engineering Construction Corporation (CCECC) ya gina, ta ratsa kogin Nun, wani reshe na kogin Neja.

Gadar wadda ita ce mafi girma a jihar Bayelsa, tana da matukar muhimmanci wajen hade babban birnin jihar Bayelsa, wato Yenagoa, da shalkwatar karamar hukumar kudancin Ijaw, wato Oporoma.

Ga mazauna yankin kudancin Ijaw, muhimmancin wannan gada tana da ma’ana ta musamman, domin wannan yanki mai cike da koguna da rafuka ya dade yana dogara sosai kan hanyoyin ruwa domin zirga-zirga, wanda ke haifar da wahalar tafiya da tsadar jigilar kaya, inda hakan yake kawo cikas ga ci gaban tattalin arzikin yankin.

ADVERTISEMENT

Amma Gadar Oporoma ta daidaita wannan matsala, kana ta inganta aikin jigilar amfanin gona da tafiye-tafiyen mazauna yankin cikin sauki.A wurin bikin kammala aikin, shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana cewa, gadar Oporoma ta inganta zirga-zirgar yankin sosai, baya ga samar da ayyukan yi da kyautata yanayin rayuwar mazauna.

Hakika, wannan misali ne na yadda hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta fannin aikin gina ababen more rayuwa ke amfanar da jama’a.Daga layin dogo na tsakanin Tanzania da Zambia zuwa gadar Oporoma, Sin ta kasance abokiyar gina Afirka mafi aminci a cikin fiye da rabin karni da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Ba tare da sanya sharuddan siyasa ba, ba tare da tsoma baki cikin harkokin cikin gida ba, Sin tana mai da hankali ne kawai kan abubuwan da jama’ar kasashen Afirka ke bukata da kuma ci gaban da suke nema, kuma wannan shi ne sirrin dorewa da ingancin hadin gwiwar Sin da Afirka.

Wannan gada, ba wai kawai ta hada gefen kogi biyu ba ce, har ma ta hada zukatan mutanen Sin da Afirka. Yayin da motoci ke ta zirga-zirga a kan gadar Oboroma, kuma musayar al’amura tsakanin gefen biyu ke kara yawaita, an yi imani cewa: Abotar Sin da Afirka tana da karfi kamar wannan gada, kuma makomar hadin gwiwar Sin da Afirka za ta kara haske.(Marubuci: MINA)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Sulaiman
    Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping
  • Sulaiman
    Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping
  • Sulaiman
    Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Wike Ya Caccaki Atiku, Ya Ce Zai Sake Tsayawa Takara A 2031 Tun Da Ya Saba

Wike Ya Caccaki Atiku, Ya Ce Zai Sake Tsayawa Takara A 2031 Tun Da Ya Saba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.