ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato

by Sadiq
11 months ago
Sakkwato

An ceto mutane 11 da ‘yan bindiga suka sace a ƙauyen Kaibaba, Gundumar Turba da ke ƙaramar hukumar Isa a Jihar Sakkwato.

Waɗanda aka ceto sun haɗa da mata bakwai, jarirai uku da matashi ɗaya.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

Jami’an tsaro ne suka gano su a dajin da ke ƙaramar hukumar Zurmi a Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato, Alhaji Idris Mohammed Gobir, ya karɓi waɗanda aka ceto a gidan gwamnati, inda ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu da jarumtarsu.

Ya ce gwamnatin Jihar  ƙarƙashin jagorancin Gwamna Ahmed Aliyu ba za ta gaji wajen yaƙi da rashin tsaro a jihar ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

Gobir ya bayyana cewa kowanne daga cikin waɗanda aka ceto zai samu Naira 100,000, buhun gero ɗaya da buhun masara ɗaya a matsayin tallafi.

Shi ma da yake magana, Shugaban ƙaramar hukumar Isa, Alhaji Sherifu Abubakar Kamarawa, ya gode wa gwamnatin jihar bisa taimakon da ta bayar, yana mai cewa hakan ya nuna damuwar gwamnati kan tsaron rayuka da jin daɗin al’umma.

MASU ALAKA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Kwankwaso
Labarai

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Next Post
EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

June 9, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026
Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

Sin Ba Za Ta Kyale Japan Da Philippines Su Take Hakkokinta Na Ruwa Ba

June 9, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.