Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin gina gidaje 20,000 a duk shekara, yayin da ta ce kusan gidaje 15,000 na kan matakai daban-daban na kammalawa a faɗin ƙasar nan. Haka kuma, gwamnatin ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Hukumar Raya Ƙasa ta Jamus (GIZ) domin hanzarta samar da gidaje masu araha da bunƙasa birane a Nijeriya.
Ministan Gidaje da Raya Birane, Injiniya Muttaqha Rabe Darma, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a Abuja yayin wata ganawa da tawagar Jamus ƙarƙashin jagorancin Dakta Karin Jansen, Shugabar Haɗin Gwiwa ta Ofishin Jakadancin Jamus a Nijeriya. A cewarsa, haɗin gwiwar na daga cikin ƙoƙarin aiwatar da manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman wajen samar da gidaje masu araha, da inganta ci gaban birane da gina ababen more rayuwa masu ɗorewa.
Ministan ya ce gwamnatin tarayya na ci gaba da neman hanyoyin rage ƙarancin gidaje a Nijeriya ta hanyar haɗin gwiwa da ƙungiyoyi da ƙasashen waje. Ya bayyana cewa ma’aikatar na kammala shirye-shiryen Tsarin Gidajen Jama’a (Social Housing Scheme), wanda zai ba da damar samar da gidaje masu araha a dukkan ƙananan hukumomi 774 na ƙasar. Shirin zai fi mayar da hankali kan masu ƙaramin ƙarfi, ciki har da malamai, ma’aikatan lafiya, masu buƙata ta musamman, matasa masu iyali da ‘yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje masu neman gidaje masu sauƙin samu.
Har ila yau, Darma ya sanar da cewa gwamnatin tarayya za ta fara aikin sauya fasalin aƙalla manyan unguwanni uku marasa ingantaccen tsari kafin ƙarshen shekarar 2026, a matsayin wani ɓangare na shirin raya birane.
A nata ɓangaren, Dakta Karin Jansen ta ce Jamus a shirye take ta faɗaɗa haɗin gwiwa da Nijeriya a fannonin raya birane masu ɗorewa, gine-ginen da ke rage amfani da makamashi da kuma ababen more rayuwa masu jure sauyin yanayi. Ita ma Sakatariyar Dindindin ta ma’aikatar, Dakta Shuaib Belgore, ta bayyana cewa wannan haɗin gwuiwa zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin gidaje da inganta rayuwar al’ummar Nijeriya.













