ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

by Abba Ibrahim Wada
52 minutes ago

Ɗan wasa Cristiano Ronaldo ya fashe da kuka a wasansa na ƙarshe na kofin duniya a ranar Litinin yayin da burinsa na lashe kyautar mafi girma ya ƙare da rashin nasara a hannun ƙasar Sifaniya da ci 1-0.

Kyaftin ɗin na Portugal mai shekaru 41 kuma ɗaya daga cikin fitattun ƴan wasa na duniya ya ce yanzu zai tafi ya yi tunanin abin da zai biyo baya. Ronaldo Ya lashe duk wata kyauta da ƴan ƙwallo ke da burin lashewa ya kuma buga wasa a manyan ƙungiyoyin Turai. Amma baya ga Cristiano Ronaldo akwai fitattun ƴan wasa da suka buga a matakin duniya suka kuma lashe kyaututtuka da dama amma suka kasa lashe kofin duniya musamman ganin yadda aka yi waje da tawagogin ƙasashensu daga gasar bana, kuma ana kyautata zaton cewa ba za su sake dawowa su fafata a gasar nan da shekara huɗu masu zuwa ba. Wasu daga cikinsu ma sun riga sun sanar da cewa wannan ita ce gasar kofin duniyarsu ta ƙarshe.

Ronaldo – Portugal

ADVERTISEMENT

A ranar Litinin bayan da Portugal ta sha kashi a hannun Spain da ci 1-0. Tauraron ɗan wasa Cristiano Ronaldo na Portugal yana da shekaru 21 lokacin da ya fara buga gasar cin kofin duniya. Wannan gasar ta kasance ta shida – wani abin da shi da Lionel Messi na Argentina kaɗai suka iya yin hakan.

Yayin da yake da shekaru 41, Ronaldo shi ne ɗan wasa na biyu mafi tsufa a gasar cin kofin duniya ta wannan shekarar. Duk da haka, ya zura ƙwallaye uku – wanda ya tabbatar da cewa har yanzu yana da rawar da yake iya takawa a fagen ƙwallon ƙafa na duniya. Kawo yanzu Ronaldo ya koma gida ba tare da ya lashe kambun gasar cin kofin duniya ba.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Fitaccen ɗan wasan na Portugal ya shafe shekaru sama da ashirin, yana hanƙoron lashe kofi ɗaya da ya bayyana a fili a matsayin babban burinsa. Bayan gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2022, Ronaldo ya yarda cewa daga kyautar da ya fi so a ƙwallon ƙafa ita ce “burinsa mafi girma.” Sai dai wannan mafarkin ya ƙare yanzu, kuma bisa ga dukkan alamu kambun gasar cin kofin duniya ya kuɓuce wa ɗaya daga cikin manyan fitattun ƴan wasan ƙwallon ƙafa na duniya, wanda za a daɗe ba a manta rawar da ya

taka wajen nishadantar da masoya ƙwallon ƙafa ba.

Neymar – Brazil

Burin Neymar na lashe gasar kofin duniya ya ƙare cikin baƙin ciki yayin da tauraron na Brazil ya fashe da kuka bayan da Norway ta fitar da zakarun gasar kofin duniya sau biyar a zagaye na ƴan16 a filin wasan New York New Jersey. Hotunan da aka nuna a talabijin sun nuna Neymar yana kuka ba ƙaƙƙautawa bayan kayen da Brazil ta sha da ci 2-1. Wannan hoto ya zame mai tayar da hankali, ba wai kawai saboda Brazil ta fice

daga gasar cin kofin duniya ba, amma saboda wataƙila wannan shi ne lokaci na ƙarshe da za a ga Neymar a babban matakin ƙwallon ƙafa.

Baya ga zama babban ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Brazil, Neymar ya ci ƙwallo sama da 100 a ƙungiyoyi uku daban-daban: Santos, Barcelona da Paris Saint-Germain. Tsohon ɗan wasan Brazil Romario da Cristiano Ronaldo ne kawai suka cimma irin wannan bajinta a ƙwallon ƙafa ta zamani ta maza, amma Neymar shi ne na farko da ya yi hakan a nahiyoyi uku daban-daban.

Neymar ɗan wasa ne mai matuƙar baiwa inda ya lashe kofunan lig a Spain da Faransa da kuma lashe gasar zakarun Turai ta UEFA a 2015.

Luka Modric – Croatia

Luka Modric da Croatia sun sha kashi a gasar cin kofin duniya ta 2026 a hannun Portugal. Wannan rashin nasarar nan take ta haifar da rashin tabbas game da makomar shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na duniya mai shekara 40.

Amma, kamar yadda ya ambata kafin gasar cin kofin duniya, hakan ya tabbatar da ritayar Luka Modri daga buga wa Croatia wasa, bayan ya tabbatar da matsayinsa na gwarzon ɗan wasa a tarihin ƙwallon ƙafa wanda ya taimaka wa Real Madrid ta mamaye fagen ƙwallon ƙafa a Turai, kuma ya jagoranci Croatia zuwa ƙololuwar fagen ƙwallon ƙafa na duniya.

Bayan zaman da ya yi a Real Madrid inda ya lashe kyautuka dama da kuma zaman da ya yi a AC Milan a kakar wasa da ta gabata, Modric ya yanke shawarar rataye takalmansa a hukumance.

Modric wanda nan ba da jimawa ba zai cika shekaru 41 ya lashe manyan kofuna da dama a lokacin da yake buga wasa a Real Madrid. Sannan shi ne wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or ta 2018 wanda ya karya mamayar da Lionel Messi da Cristiano Ronaldo suka yi wa kyautar na tsawon shekaru 10.

Har ila yau, Modric ya lashe gasar zakarun Turai sau shida, kuma ya lashe manyan kofuna 28, wanda ya sanya ya zama ɗan wasa mafi lashe kyautuka da ya taɓa saka rigar Real Madrid.

Riyad Mahrez – Algeria

Shima ɗanwasa Riyad Mahrez ya sanar da yin ritaya daga buga wa Algeria wasa bayan da Algeria ta sha kashi a hannun Switzerland da ci 2-0 a zagayen ƴan 32 na gasar cin kofin duniya ta 2026. Tsohon ɗan wasan na Manchester City ya bayyana cewa ya shafe shekaru 12 yana buga wa ƙasarsa wasa, wanda ya haɗa da lashe gasar kofin nahiyar Afrika (AFCON).

Mahrez ya sanar da hakan ne a lokacin da yake magana da kafar yaɗa labarai ta beIN SPORTS bayan da aka fitar da Algeria daga gasar. Ya ce rashin nasarar da aka samu a gasar cin kofin duniya ya kawo ƙarshen wasansa na ƙasa da ƙasa bayan shafe fiye da shekara 10 yana wakiltar ƙasarsa inda ya buga wasanni 119.

Edin Dzeko – Bosnia

Za a iya cewa yan wasa ƙalilan ne kawai za su iya goga kafaɗa da ɗan wasan Schalke Edin Džeko ta fannin cin ƙwallaye. Ɗan wasan dai ya murmure daga raunin da ya yi fama da shi ya kuma taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da matsayin ƙasarsa a gasar. Džeko, ɗan wasan Bosnia mafi hazaƙa da yawan zura ƙwallaye, ya shafe shekara 20 yana buga ƙwallo a matakin mafi girma a fagen ƙwallon ƙafa a duniya. Ɗan wasan mai shekaru 40 ya nuna cewa har yanzu yana iya buga wasa a matakin mafi girma. na Dzeko, wanda ya buga wa tawagar ƙasarsa wasa 148, ya buga wasanni bakwai daga cikin takwas da ƙasarsa ta yi a rukunin H na neman gurbin shiga gasar ta bana. ƙwallo 65 da ya ci sun tabbatar da shi a matsayin ginshiƙi a tarihin ƙwallon ƙafa na ƙasarsa.

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
  • Abba Ibrahim Wada
    LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

MASU ALAKA

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
Wasanni

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Wasanni

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA
Wasanni

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Next Post
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.