Jami’an tsaron sun yi wata fafatawa mai zafi da wani gungun miyagun ƴan bindiga da yawansu ya kai kusan 240 a yankin kan iyakokin Jihohin Zamfara da Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga watan Agusta, 2026, domin daƙile yunƙurinsu na cin karensu babu babbaka a yankin.
Kamar yadda bayanan da aka tattara suka tabbatar, ƴan bindigar sun ɓullo ne daga wata maɓoya da ake kira Sangeko Gap a Jihar Zamfara, inda suka nufi garin Makuku da ke cikin Jihar Kebbi. Nan take dakarun sojoji na Bataliya ta 3 (COAS Intervention Battalion 3) ƙarƙashin Divishin na 8, tare da dakarun sojin sama na Operation FANSAR YAMMA da jami’an ƴansanda makwantar da tarzoma (Mobile Police Force) suka tari gabansu da luguden wuta.
Wani ganau mai suna Fua’ad Bello ya bayyana cewa maharan sun rabu gida uku ne a lokacin da suke gudanar da wannan ta’addanci. Wannan mummunan yanayi ya sanya mazauna garuruwan da ke kewaye shiga cikin mawuyacin hali, inda tuni jama’a suka fara ficewa daga muhallansu zuwa yankunan da ke da ɗan dama-dama domin neman mafaka yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da ruwan harsasai.
Wani jami’in ɗansanda da ke aiki a yankin ya tabbatar da cewa babbar manufar tura waɗannan dakarun haɗin gwiwa ita ce don hana ƴan bindigar samun gindin zama ko shiga wasu ƙauyukan da ke kusa su aika ta ɓarna. Ya kuma buƙaci al’ummar yankin da su ci gaba da kasancewa cikin taka-tsantsan tare da bin umarnin jami’an tsaro har sai an kammala aikin kakkaɓe maharan gaba ɗaya.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto a yammacin ranar 10 ga watan Agusta, 2026, hukumomin tsaro ba su su fitar da wata ƙididdiga ta hukuma ba dangane da adadin waɗanda suka rasa rayukansu ko suka raunata daga ɓangarorin biyu ba.














