A yau Jumma’a, mai magana yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana cewa, kasar Sin ta nuna rashin jin dadinta ga Italiya da Kungiyar Tarayyar Turai (EU) game da ziyarar da wasu ‘yan siyasa masu rajin wai “samun ‘yancin kan Taiwan” suka kai Italiya domin halartar wani taro.
Mao ta bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai na yau da kullum, sa’ilin da aka nemi ta yi tsokaci kan ziyarar da ‘yar siyasar Taiwan, Hsiao Bi-khim, ta kai Italiya.Mao ta ce, “Shugabannin jam’iyyar DPP da wasu ‘yan siyasa suna amfani da dabaru na makirci iri-iri domin su yayata kansu a kafofin watsa labarai.”
Yayin da take nuni da cewa, ‘yan siyasar suna neman samun ‘yancin kai ta hanyar hada kai da wasu bangarori na waje a karkashin wai kalmomin “dimokuradiyya” da “‘yancin kai”, Mao ta bayyana cewa irin wadannan ayyuka abin a yi tir ne kuma a karshe za su zama na banza.
Mao ta jaddada cewa, kasar Sin kwara daya ce tal a duniya, kuma Taiwan wani bangare ne na yankin kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba.
A cewar Mao, kodayaushe, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen nuna adawa da duk wani nau’i na yin mu’amala a hukumance tsakanin yankin Taiwan na Sin da kuma kasashen da suka kulla dangantakar diflomasiyya da kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














