Jami’in kula da shirye-shirye a hukumar kula da harkokin tattalin arzikin Afirka ta MDD (UNECA), Batanai Clemence Chikwene, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin a kwanan nan cewa, matakin da kasar Sin ta dauka na soke biyan haraji ga kayayyakin Afirka da ake shigo da su kasarta, wani abu ne na lale marhabin, kuma ya bai wa kasashen nahiyar damar cin moriyar kasuwannin kasar Sin mai fiye da adadin mutane biliyan 1 da ke da manufa mai kyakkyawan tsari mara tangarda.Chikwene ya shaida wa Xinhua cewa, “Manufar ta nuna sha’awar kasar Sin kan taimaka wa kasashen Afirka su bullo da hanyar fita daga kangin talauci ta kashin kansu, da kuma fara hawa turbar samun wadata.
Hakan yana kuma rage shingen shiga kasuwannin kasar Sin, kana yana ba da damammaki na hakika ga ’yan kasuwa na Afirka da za su yi amfani da su a matsayin turbar samun ciniki da wadata.”Jami’in na hukumar UNECA ya kara da bayyana cewa, sabanin tsoffin kasuwannin da Afirka ta saba kai kaya a ketare, yanayi ko tsarin manufa a kasar Sin ba shi da tangarda, kuma masu fitar da kayayyaki na Afirka ba za su fuskanci karin kudin harajin kwastam ba ko kuma bullo da wasu bukatu na ba-zata.
Chikwene ya jaddada cewa, ya kamata gwamnatocin kasashen Afirka su tsara manufofin tallafawa, sannan su kuma kamfanonin Afirka su fitar da kayayyakin da suke da ingancin da ya dace, domin cin gajiyar manufar soke harajin ta kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post