A gundumar Gyirong ta birnin Xigaze a jihar Xizang mai cin gashin kanta ta kasar Sin, inda ibtila’in zaftarewar kasa da ya abku a kasar Nepal kwanan nan ya shafa, ana ci gaba da gudanar da ayyukan ceto.
A cewar Luobu Ciren, mukaddashin magajin garin Xigaze, an tura ma’aikatan ceto sama da 2,300 da na’urori sama da 8,800 zuwa yankin da ibtila’in ya fi shafa. Kuma an gano gawarwakin mutane 31, yayin da har yanzu akwai mutane 531 da ba a gano inda suke ba.
Bugu da kari, a jihar ta Xizang, an bude layin waya na hidima ga iyalan mutanen da suka bace, domin amsa bukatun jama’a yadda ya kamata, da kuma tattara bayanai daidai.
Haka kuma, kasar Sin ta samar da taimako ga bangaren Nepal. Kwanan nan, Sharachchandra Bhandary, babban editan kamfanin dillancin labarai na kasar Nepal, ya bayyana cewa bayan abkuwar ibtila’in, kasar Sin ta ba Nepal kayan aikin ceto, da kayayyakin jinya da sauran kayayyaki masu alaka da su, da kuma tallafin kudi, sannan ta taimaka wajen maido da harkokin sufuri a yankin da ibtila’in ya shafa. (Bilkisu Xin)














