Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta fitar da gargaɗi ga al’ummar ƙasa baki ɗaya, musamman jihohi 12, kan tsananin zafi da ke ƙaruwa, inda ta ce yanayin na iya haddasa matsalolin lafiya masu alaƙa da zafin rana.
Jihohin da NiMet ta lissafo sun haɗa da Neja, Kebbi, Sokoto, Zamfara, Katsina, Kano, Yobe, Jigawa, Bauchi, Gombe, Borno da Adamawa.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na intanet, ta ce ƙarin zafin da ake samu a faɗin Nijeriya na iya jefa mutane cikin haɗarin lafiya, musamman mazauna jihohin Arewa.
Hasashen ma’aunin zafi ya nuna cewa wasu sassan Arewa, Tsakiyar Nijeriya da Kudancin ƙasar za su fuskanci matsanancin zafi.
Ana sa ran yanayin zafin zai kai: Jihohin Arewa: tsakanin 40 zuwa 45°CJihohin Tsakiya: tsakanin 35 zuwa 38°CJihohin Kudu: tsakanin 33 zuwa 35°C.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa har ma jihohin da ba a ambata ba na iya fuskantar tasirin wannan zafi.















Discussion about this post