Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta samu tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, da laifi kan tuhume-tuhume guda 12 da suka shafi yaudara da karkatar da kudaden aiki da Hukumar EFCC ta shigar a kansa.
Yayin yanke hukunci a ranar Alhamis, Mai Shari’a James Omotosho ya ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da zargin da ake yi wa tsohon ministan ba tare da wata shakka ba.
Kotun ta same shi da laifi a dukkan tuhume-tuhumen da ke cikin shari’a mai lamba FHC/ABJ/CR/273/2024.
An samu Mamman, wanda ya yi aiki a gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, da laifin karkatar da kuɗaɗen gwamnati da suka kai kusan naira biliyan 33.8 ba bisa ƙa’ida ba.
“Ba abin mamaki ba ne yadda har yanzu ‘yan Nijeriya ke cikin duhu,” in ji alkalin yayin yanke hukuncin.
Sai dai wanda ake tuhuma bai halarci zaman kotun ba yayin sauraron tuhume-tuhumen.
Kotun ta sanya ranar 13 ga Mayu, 2026 domin yanke masa hukunci.















Discussion about this post