A daidai lokacin da ake bikin ranar ‘yan kwadago ta duniya ta bana, babban sakataren kwamitin koli na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin(JKS), kuma shugaban kasar Xi Jinping ya mika sakon barka da kuma fatan alheri ga ma’aikatan kasar.
Tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, ko da yaushe shugaba Xi na mayar da hankali kan ma’aikatan kasar, kuma ya sha nuna yabo ga ma’aikatan da suke kasancewa ababen koyi, bisa ruhinsu da kuma kwarewarsu.
Ya kuma karfafa ma’aikata a kan su himmatu wajen yin kirkire-kirkire, da jajircewa wajen fafutuka, da kuma jagorantar duk al’ummar kasar wajen daukaka darajar aiki, muhimmancin kirkire-kirkire. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post