Wani dan bautar kasa, Abdulsamad Jamiu, ya rasa ransa bayan ya shiga tsakiyar musayar wuta tsakanin sojoji da wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne a yankin Dei-Dei da ke Abuja.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Asabar a unguwar Shagari E da ke yankin.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar soji, Odunola Olawuyi, ya fitar a ranar Lahadi, ya ce sojojin rundunar Kuick Response Group suna sintiri na dare ne lokacin da suka karbi kiran gaggawa kan harin fashi da makami.
Ya ce da zuwansu wurin, ‘yan fashin da ke gudu suka bude musu wuta, wanda ya haifar da musayar wuta tsakanin bangarorin biyu.
A cikin wannan musayar wuta ne Abdulsamad Jamiu ya tsinci kansa cikin harsasai.
Rundunar sojin ta bayyana cewa duk da kokarin da sojoji suka yi na tabbatar da tsaro da kare jama’a, dan bautar kasar ya rasu sakamakon raunin da ya samu.
Sojojin sun bayyana lamarin a matsayin abin takaici, suna masu cewa yanayin lokacin ya kasance mai tsanani yayin da ake kokarin fatattakar ‘yan fashin tare da kare mazauna yankin.
Kwamandan Rundunar Guards Brigade, hafsoshi da sojoji sun mika sakon ta’aziyyarsu mai zurfi ga iyalan marigayin, NYSC, da kuma duk wadanda wannan babban rashi ya shafa. Sun ce suna tare da su cikin wannan bakin ciki mai tsanani.
Sanarwar ta kara da cewa an kai gawar mamacin Asibitin Gwamnati na Kubwa a Babban Birnin Tarayya.
Rundunar sojin ta kuma bayyana cewa an fara bincike domin gano ainihin yadda lamarin ya faru, tare da tabbatar da cewa za a bayyana sakamakon binciken ga jama’a.
Haka kuma rundunar ta ce tana nan daram wajen jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a Babban Birnin Tarayya.
Ta kara da cewa za ta ci gaba da duba hanyoyin gudanar da ayyukanta domin kara inganta tsaron fararen hula, yayin da dakarunta ke ci gaba da fuskantar masu aikata laifi da ke barazana ga zaman lafiyar al’umma.
An bukaci mazauna yankin su kwantar da hankalinsu tare da ba hukumomin tsaro cikakken hadin kai.
Da yake mayar da martani kan lamarin, wata kafar da ke bibiyar ayyukan soja da tsaro a Nijeriya mai suna Nigerian Armed Forces Diary, ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Lahadi, inda ta yi Allah-wadai da abin da ya faru tare da kira da a gudanar da gaggautaccen bincike.
Kafar ta ce: “Wannan matashin da kuke gani a hoton nan ya rasu! Har zuwa rasuwarsa, yana cikin masu yi wa kasa hidima na NYSC. A cikin dakin sa da ke Shagari Kuarters, Dei-Dei, Abuja, jami’an sojoji sun harbe shi har ya rasa ransa, suna ikirarin cewa ‘kuskure ne’.
“Marigayi Samad ba don laifi ba ne. Yana kawai yi wa kasarsa hidima ne, amma ya rasa ransa a hannun wadanda aka dauka domin kare shi.
“Muna bukatar shugabancin soja ya gaggauta bincike kan wannan lamari, a hukunta wadanda ke da hannu, kuma a tabbatar an yi wa iyalansa adalci. Allah ya kare irin wannan abu daga sake faruwa,” in ji sakon.
A wani labarin kuma, jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa a ranar 23 ga Afrilu, an kashe wani dan bautar kasa, Ben Agir, bayan da wasu ‘yan sa-kai suka doke shi har lahira a karamar hukumar Buruku ta Jihar Benuwe .
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a yankin Anibros yayin sintirin dare da ‘yan sa-kan ke yi.
Sojoji Sun Ceto Wanda Aka Yi Garkuwa Da Shi, Sun Kuma Kwato Naira Miliyan 8 A Filato
Rahotanni sun bayyana cewa aikin ceto ya biyo bayan samun bayanan sirri da dakarun soji suka yi amfani da su wajen kai farmaki ga maboyar masu garkuwa da mutane.
Sojojin sun kuma yi nasarar kama wasu daga cikin wadanda ake zargi da aikata laifin, yayin da ake ci gaba da bincike domin kamo sauran mambobin kungiyar.
Rundunar ta jaddada kudirinta na ci gaba da yaki da masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka, tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.
Dakarun Operation Enduring Peace sun ceto wata da aka yi garkuwa da ita tare da kwato Naira miliyan 8 da aka biya a matsayin kudin fansa a Karamar Hukumar Kua’an Pan ta Jihar Filato .
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar hadin gwiwa ta Operation Enduring Peace, Kyaftin Chinonso Polycarp Oteh, ya sanya wa hannu a ranar Lahadi.
Sanarwar ta ce an gudanar da aikin ne a ranar Asabar, 25 ga Afrilu, 2026, inda dakarun da ke Sektor 9 Shendam suka yi nasarar ceto wanda aka yi garkuwa da shi tare da kwato kudin fansa da iyalansa suka biya.
A cewar sanarwar, an yi garkuwa da matar ne a ranar 19 ga Afrilu, 2026, a yankin Bauna da ke karamar hukumar Shendam.
Ta kara da cewa ta hanyar tattara bayanan sirri da kuma tambayar wani da aka kama wanda ya amsa laifin, dakarun sun gano inda aka boye ta a dajin Padam da ke Karamar Hukumar Kua’an Pan, inda suka same ta suka ceto ta.
Sojojin sun kuma bayyana cewa an kwato kudin fansa da aka biya wato Naira miliyan 8, wanda aka mayar wa iyalan wanda aka sace bayan ceto ta.
Bayan an ceto ta, an kai ta asibitin gwamnati na Shendam domin duba lafiyarta kafin daga bisani a mika ta ga iyalanta.
Sanarwar ta kuma ce dakarun na ci gaba da gudanar da bincike da farmaki a maboyar ‘yan garkuwa da mutane a yankin Kua’an Pan da Shendam domin kama sauran mambobin kungiyar.
Rundunar ta kuma yabawa jama’a bisa hadin kai, tare da kira a ci gaba da bayar da bayanai cikin gaggawa domin taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.















Discussion about this post