Yayin da rikicin Amurka da Isra’ila da Iran ya kara haifar da barazanar tsaro da ke tattare da tsoffin hanyoyin jiragen ruwa, wasu kafafen yada labaru na sassan kasa da kasa, ciki har da jaridar Daily Mirror ta kasar Sri Lanka, da kafar labarai ta shafin intanet mai suna Observatorio de la Política China ta kasar Sifaniya, sun yaba da tashoshin jiragen ruwa da kamfanonin kasar Sin suka gina, da zirga-zirgar jiragen kasa tsakanin kasar Sin da Turai, inda suka bada shawarar sake yin tunani kan alfanu gami da ma’anar raya shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin hadin gwiwa, wadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bullo da ita.
Jaridar Daily Mirror ta ruwaito cewa, yawaitar rikicin yankin Gabas ta Tsakiya ta taimaka ga ci gaban harkokin tashar jiragen ruwa ta kasa da kasa ta Hambantota da ke kudancin kasar Sri Lanka, tashar da ta kasance wani muhimmin aikin hadin gwiwar Sin da Sri Lanka a bangaren raya shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.
Tsakanin watan Janairu zuwa Maris din bana, yawan hajojin da aka shigo gami da fitar da su tashar, ya zarce tan miliyan 2.01, adadin da ya karu da kaso 47 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara.Tun bayan da shugaba Xi Jinping ya bullo da ra’ayin raya shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin hadin gwiwa a shekara ta 2013, ya zuwa yanzu, shawarar ta riga ta karade kasashe sama da 150 da kungiyoyin kasa da kasa sama da 30.
Ita kuwa kafar labarai ta shafin intanet ta Observatorio de la Política China ta kasar Sifaniya ta wallafa wani bayani ne da ke cewa, raya shawarar Ziri Daya da Hanya Daya cikin hadin gwiwa, ya sauya ajandar kasar Sin bisa manyan tsare-tsare zuwa babban tsarin hadin gwiwa mai kunshe da muhimman ababen more rayuwa, da kara mu’amalar mabambantan sassa, da cinikayya da kere-kere da sauransu, al’amarin da ya zama babban karfin dunkule shiyyar da ma duk duniya baki daya. (Murtala Zhang)















Discussion about this post