Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, a yau ran 15 ga watan Mayu, ya amsa tambayoyin ‘yan jarida game da ziyarar shugaban Amurka Donald Trump a nan kasar Sin.
Wani dan jarida ya tambaya cewa, a jiya 14 ga watan Mayu, shugaba Xi ya shirya jerin ayyuka na ziyarar aiki ga shugaban Amurka Trump da ya zo ziyara a kasar Sin, wanda hakan ya ja hankalin mutane cikin gida da wajen kasar sosai.
Ko bangaren Sin zai iya bayar da karin haske game da wannan lamari?Kakakin ya bayyana cewa, bisa gayyatar da shugaba Xi ya yi masa, shugaban Amurka Donald Trump ya gudanar da ziyarar aiki a Sin.
Wannan shi ne ganawar ta farko da shugabannin kasashen biyu suka yi na ido-na-ganin-ido tun bayan taron koli na Busan a watan Oktoba na shekarar da ta gabata, kuma ita ce ziyarar da shugaban Amurka ya sake kawowa Sin cikin shekaru 9 da suka gabata.
A ranar 14 ga watan Mayu, shugaba Xi ya shirya liyafar maraba ga shugaba Trump, ya gudanar da tattaunawa da shugaba Trump, tare da ziyartar wurin ibada na Tiantan. Shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi masu zurfi kan manyan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da kuma duniya, kuma sun cimma sabbin yarjejeniyoyi da dama.
Kakakin ya ce, shugabannin kasashen biyu sun amince da kafa “dangantaka mai dorewa da amfani bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Amurka”, matakin ya zama sabon matsayi na dangantakar kasashen biyu, wanda zai zama jagora mai hangen nesa ga dangantakar Sin da Amurka cikin shekaru 3 masu zuwa har ma a nan gaba, kana zai ciyar da dangantakar kasashen biyu gaba cikin kwanciyar hankali, da ci gaba mai dorewa ba tare da tangarda ba, da kuma kawo karin zaman lafiya, wadata da ci gaba ga duniya.
Kakakin ya kara bayyana cewa, shugabannin kasashen biyu sun kuma cimma muhimmiyar yarjejeniya kan magance abubuwan dake jawo hankulansu yadda ya kamata, kuma sun amince da karfafa tattaunawa da daidaita batutuwan shiyya-shiyya da na kasa da kasa. (Amina Xu)














Discussion about this post