Jam’iyyar ta amince da tsayar da tsohon mataimakin gwamnan jihar Sokoto, Manir Muhammad Dan-Iya, a matsayin ɗan takararta na gwamna domin zaɓen shekarar 2027.
Dan-Iya, wanda ya kasance mataimakin tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal daga 2018 zuwa 2023, ya samu tikitin takarar ne ta hanyar sulhu bayan sauran ‘yan takara 10 sun amince su mara masa baya domin jagorantar jam’iyyar zuwa zaɓe.
Ana sa ran babbar fafatawar zaɓen gwamnan 2027 a jihar za ta kasance tsakaninsa da gwamna mai ci Ahmad Aliyu na jam’iyyar APC.
A cikin wata sanarwa da tsohon kakakinsa ya fitar, Dan-Iya ya gode wa Sanata Tambuwal bisa goyon baya, da haɗin kai da rawar da ya taka wajen bunƙasa siyasa a jihar. Ya ce goyon bayan da yake samu daga dattawa, da matasa, da ƙungiyoyin mata da abokan hulɗarsa na siyasa na nuna haɗin kai domin inganta makomar jihar.
Manir Muhammad Dan-Iya, wanda ya fito daga ƙaramar hukumar Kware, ya taɓa riƙe muƙamai da suka haɗa da shugaban ƙaramar hukumar Kware, da babban mataimaki na musamman ga tsohon kakakin majalisar wakilai Tambuwal, da kuma kwamishinan ƙananan hukumomi a gwamnatin jihar.
A zaɓen 2023, Dan-Iya wanda ke riƙe da sarautar Walin Sakkwato, ya nemi kujerar Sanatan Sakkwato ta Tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar PDP amma ya sha kaye a hannun Sanata Aliyu Wamakko.














Discussion about this post