Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce kalaman da ake ji daga mahukuntan kasar Japan masu sabawa ayyukan kasar na zahiri, ba za su kwantar da hankulan sassan kasa da kasa dangane da yunkurin farfado da karfin sojinta ba.
Mao Ning, wadda ta bayyana hakan a Talatar nan yayin taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da take amsa wata tambaya mai nasaba, ta ce a shekarun baya-bayan nan, gwamnatin Japan ta ci gaba da fadada kasafinta na ayyukan soja, da sassauta takunkuman dake kan kasar a fannin fitar da makamai masu hadari, da shiga atisayen soji na hadin gwiwa, da bunkasa girke makamai masu linzami dake iya cin dogon zango.
Kazalika, kasar na gina abun da ta kira “Garkuwar hare-hare”, mai nasaba da yaki na kai tsaye, tana kuma tara dunbin sinadaran sarrafa nukiliya, da ingiza manufar sake nazartar kundin tsarin kasar dangane da matakan danniya, da gabatar da shawarar mayar da kasar mai karfin ikon shiga yaki, kana tana ci gaba da keta dokokin cikin gida da na kasa da kasa.
La’akari da dukkanin wadannan, Mao ta ce kasar Sin na kira ga bangaren Japan da ya koyi darasi daga tarihi, ya martaba alkawarin zaman lafiya, da janyo amincewar kasashe makwaftan kasar na nahiyar Asiya, da ma al’ummun kasa da kasa ta hanyar aiwatar da matakai na hakika. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post