Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwa ta Sin ya gudanar da taron manema labarai a yau, inda ya gabatar da bayanai game da taron shugabannin kamfanonin kasashen waje na Qingdao karo na 7.
Wani jami’in ma’aikatar kasuwanci ya bayyana cewa, a lokacin shirin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15, ma’aikatar kasuwancin za ta ci gaba da fadada bude kasuwar Sin mai zurfi ba tare da karkacewa ba, da zurfafa bude kasuwannin hidimomi, da kuma gina “sabon tsari” na bude kofa bisa ka’idojin ciniki na duniya, tare da samar da sabbin fa’idodi don jawo hankalin kamfanonin kasashen waje su zuba jari tare da habaka ayyukansu a Sin.
Ma’aikatar kasuwanci ta Sin ta bayyana cewa, a mataki na gaba, za a fadada bude kofa a fannonin hidimomi kamar su sadarwa da yanar gizo da ba da ilimi da al’adu, da kiwon lafiya, da kuma aiwatar da gwajin bude kofa a fannonin sadarwa da fasahar kwayoyin halitta da asibitoci masu jarin waje da sauransu a hankali, tare da tallafa wa kamfanonin samar da hidimomi na kasashen waje su fadada harkokinsu a nan kasar Sin. (Amina Xu)














Discussion about this post