Babban kamfanin fasahohin zamani na kasar Sin Huawei, ya sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da cibiyar horar da ma’aikata ta kasar Kenya ko KSG, da nufin sauya yanayin gudanar da ayyukan gwamnatin Kenya zuwa tsari na dijital.
Wata sanarwa da kamfanin na Huawei ya fitar jiya Laraba a birnin Nairobi fadar mulkin kasar Kenya, ta ce tsarin na hadin gwiwa tare da KSG, wanda aka sanyawa hannu a ranar Talata, zai samar da damar bunkasa hidimomin gwamnati ta hanyar kyautata kwarewa a fannin fasahohin dijital, da raba ilimi, da gudanar da shirye-shiryen hadin gwiwa don inganta makamar aiki.
Kamfanin na Huawei ya kara da cewa hadin gwiwar sassan biyu, ya yi daidai da babbar ajandar sauyi zuwa tsarin dijital na kasar Kenya, yana kuma taimakawa kokarin da ake yi yanzu haka na zamanantar da hidimomin gwamnatin kasar.
Karkashin yarjejeniyar, za a mayar da hankali ga aiwatar da shirye-shiryen bayar da horo na hadin gwiwa, da hada karfi wajen gudanar da bincike da musayar kwarewa, da taimakawa juna wajen raya kwarewar fasahohin dijital na zamani, a fannonin kirkirarriyar basira ko (AI), da tsaron intanet tsakanain ma’aikatan gwamnati.
Kazalika, karkashin yarjejeniyar, kamfanin Huawei zai taimawa wajen horar da ma’aikatan gwamnatin Kenya 2,000, da jami’an cibiyar KSG 50 tsakanin shekarar nan ta 2026 zuwa 2029 a muhimman fannoni kamar na AI da tsaron intanet. (Saminu Alhasan)















Discussion about this post