Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi watsi da zargin cewa yana yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu aiki a ɓoye.
A yayin wata hira da ya yi da gidan talabijin na Global TV a daren Laraba, Kwankwaso ya ce an daɗe ana yaɗa wannan jita-jita tun lokacin da yake jam’iyyar NNPP.
Daily Trust ta rawaito cewa, Sanusi Bature, mai magana da yawun gwamna Abba Yusuf, yayi zargin a wata hira da ya yi da Arise News a ranar Laraba cewa, Sanata Kwankwaso yana taimakawa muradun Tinubu a ɓoye gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Bature ya ce, “Akwai waɗanda ke aiki tare da Tinubu a fili, kai tsaye a bainar jama’a, sannan akwai waɗanda ke iya yi masa aiki a ɓoye.
“Na yi imanin cewa, duk abin da Kwankwaso yake yi zai amfani Tinubu a karshe saboda Kwankwaso ya yi wa Tinubu aiki a shekarar 2023.
“Ni mamba ne na APC; na kasance mai magana da yawun ’yan adawa a Kano, kuma na san abin da ya faru a 2023. Na yi imanin cewa Kwankwaso yana yi wa Tinubu aiki a ɓoye domin zaben 2027.”
Sai dai da yake mayar da martani kan zargin, Kwankwaso ya ce, “Ina ganin, marasa tunani ne kawai za su yarda da hakan. Ba ma yi wa kowa aiki. Muna yi wa NDC aiki ne kawai.
“Bola Tinubu babban yayana ne kuma aminina na kirki har zuwa yanzu. Amma hakan ba yana nufin za mu haɗa dukkan manufofinmu na siyasa da shi ba. Shi yana yin nasa, ni kuma ina yin nawa.”















Discussion about this post