Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta tantance maza da mata 720 da suka nemi shiga shirin auren gata da gwamnatin jihar ke shiryawa.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Dakta Mujahideen Aminuddeen Abubakar ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
Ya ce mutanen da aka tantance sun fito ne daga ƙananan hukumomi 24 na jihar, yayin da ake ci gaba da aikin tantancewar.
Dakta Abubakar ya buƙaci waɗanda suka karɓi fom ɗin shiga tsarin auren daga hedikwatar Hisbah da su kai fom ɗinsu da aka cike tare da sakamakon gwajin lafiya zuwa ofishin SAKA domin ci gaba da tantance su.
Ya kuma ce za a sanar da ranakun tantance waɗanda suka fito daga sauran ƙananan hukumomin jihar a nan gaba.
An tsara shirin auren gatan ne domin taimaka wa kusan mutum 3,000 wajen rage musu nauyin hidimar aure tare da inganta zaman lafiya da ɗorewar iyali a jihar.














Discussion about this post