Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta ƙaryata rahotannin da ke cewa ‘yan bindiga sun kai hari a wasu makarantu a jihar.
Jita-jitar ta yaɗu a ranar Laraba, lamarin da ya haifar da fargaba a tsakanin jama’a, inda aka ce an kai hari makarantu a Bosso, Chanchaga, Kpakungu, Sabon-Wuse da Lambata.
Sai dai kakakin ‘yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun, ya ce labarin ba gaskiya ba ne.
Ya ce jami’an ‘yansanda sun ziyarci dukkanim makarantu da aka ambata, kuma sun tabbatar cewa babu wani hari da aka kai.
Ya buƙaci jama’a da su yi watsi da jita-jitar, yana mai cewa an ƙirƙira ta ne domin tayar da hankalin jama’a da haifar da tsoro a makarantu da unguwanni.
Ya kuma tabbatar da cewa yanayin tsaro a waɗannan wurare na nan lafiya.














Discussion about this post