Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sanar da naɗa Daniel Ogunmodede, mataimakin kocin Super Eagles, a matsayin sabon kocin ƙungiyar domin jagorantarta a kakar wasa ta 2026/2027.
Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce ta cimma yarjejeniya da Ogunmodede kan jagorantar ƙungiyar.
Kafin wannan naɗi, ana ta hasashen wanda zai zama sabon kocin Kano Pillars gabanin fara sabuwar kakar wasa.
Ogunmodede mai shekaru 46 ana sa ran zai sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyu.
Sabon kocin ya jagoranci a baya Remo Stars, inda ya jagoranci ƙungiyar ta lashe Gasar Firimiyar Nijeriya a kakar wasan 2024/2025.
Baya ga haka, yana cikin masu taimaka wa kocin Super Eagles, Eric Chelle, kuma ana kallonsa a matsayin ɗaya daga cikin matasan masu horar da ƙwallon ƙafa mafi ƙwarewa a Nijeriya.
Magoya bayan Kano Pillars na fatan sabon kocin zai kawo sauyi tare da mayar da ƙungiyar kan turbar nasara bayan gaza yin kataɓus a kakar bana da ta ƙare.
Ana sa ran Kano Pillars za ta gabatar da Ogunmodede a hukumance cikin kwanaki masu zuwa, yayin da ƙungiyar ke ci gaba da shirye-shiryen tunkarar kakar wasan 2026/2027.














