ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Abinci: Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Sansanin Soji A Tafkin Chadi

by Sadiq
2 years ago
Abinci

Gwamnatin Tarayya na shirin kafa rundunar soji mai karfi a yankin tafkin Chadi, domin inganta samar da abinci a Nijeriya.

Gwamnan Jihar Borno Babagana Umara Zulum ne, ya bayyana hakan bayan wata ganawa da ya yi da shugaban kasa Bola Tinubu, a fadar shugaban kasa da ke Abuja, a ranar Talata.

  • A Kawo Ɗauki Don Magance Tsadar Kuɗin Zuwa Aikin Hajjin Bana
  • Kwamandojin Boko Haram 2 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

Shirin na son farfado da aikin noman rani a yankin tafkin Chadi, wanda ke samar wa Nijeriya abinci mai yawan gaske, amma hakan ya durkushe sakamakon ayyukan ta’addancin Boko Haram da ya shafe sama da shekaru 10.

ADVERTISEMENT

“Yanzu da zaman lafiya ya samu a Jihar Borno akwai bukatar gwamnati ta tabbatar da sake farfado da noman rani a yankin Chadi ta Kudu.

“Na yi magana da shugaban kasa, kuma zai duba yiwuwar kafa rundunar tsaro a yankin tafkin Chadi domin mutane su samu damar zuwa gonakinsu domin yin noma,” in ji Zulum.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Gwamnan ya jaddada aniyar farfado da noman rani a yankin Chadi ta Kudu da ke Arewacin Borno, don magance matsalar karancin abinci da al’ummar kasar nan ke fuskanta.

Zulum ya kuma bayyana cewa ‘yan Nijeriya mazauna kasashen Chadi, Jamhuriyar Nijar, da Kamaru da aka dakatar da dawowa gida sakamakon zabe da damina, za su dawo gida karkashin jagorancin shugaba Tinubu.

Dangane da batun tsaro a makarantu, Zulum ya bayyana cewa, yanzu haka an girke sojoji, Cvilian JTF, mafarauta da kuma ’yan banga a makarantun jihar don bai wa dalibai tsaro.

Gwamnan ya ce a halin da ake ciki gwamnatinsa ta dawo da sama da mutane 100,000 da suka rasa muhallansu zuwa Borno cikin shekaru shida zuwa bakwai da suka wuce, kuma ana sa ran samun karin wasu nan gaba.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
CBN Ya Kara Adadin Kudin Ruwa Zuwa Kashi 24.75

CBN Ya Kara Adadin Kudin Ruwa Zuwa Kashi 24.75

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.