Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin ta samar da cikakken tsarin ayyukan masana’antu, da yanayin aiwatarwa mai nagarta, da isasshen adadi na kwararru, tana kuma kara inganta manufofi masu samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kirkire-kirkire domin cimma gajiyar masana’antun kasa da kasa.
Lin Jian, ya bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da yake amsa tambayar da aka yi masa game da sakamakon wani binciken baya-bayan nan, wanda ya nuna yadda kaso 80 bisa dari na kamfanonin Amurka, suke kallon hada-hadar da suke gudanarwa a kasar Sin a matsayin ko dai mai matukar muhimmaci, ko mai muhimmaci, wajen bunkasa gogayyarsu a matakin kasa da kasa.
Lin, ya ce karin kamfanonin waje na zabar gudanar da ayyukan bincike da samar da ci gaba a kasar Sin, da daga darajar cibiyoyinsu na sarrafa hajoji zuwa manyan cibiyoyin kirkire-kirkire, da kyautata gogayyarsu a matakin kasa da kasa da babbar kasuwar kasar Sin.
Jami’in ya kara da cewa, Sin za ta ci gaba da karfafa bude kofa bisa babban matsayi, da kyautata gagarumin tallafinta, da gata ga kamfanonin ketare. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post