Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ‘yancin kai ga ɓangaren shari’a yayin da ya kaddamar da sabon rukunin gidaje guda 10 na Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara a yankin Katampe da ke Abuja.
Shugaban ƙasar, wanda Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, ya wakilta, ya bayyana aikin a matsayin wata muhimmiyar zuba jari da za ta ƙarfafa bin doka da oda da kuma dimokuraɗiyya a ƙasar nan.Ya ce rukunin gidajen na daga cikin jerin ayyukan gine-ginen shari’a da ake ƙaddamarwa domin bikin cika shekaru uku da gwamnatin sa ta yi a kan mulki.
A cewarsa, ingantaccen tsarin shari’a ba ya dogara ne kawai kan dokoki da alƙalai ba, har ma yana buƙatar samar da ingantattun kayayyakin more rayuwa da za su taimaka wa masu gudanar da shari’a wajen sauke nauyin da ke kansu yadda ya kamata.
Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da tallafa wa ɓangaren shari’a domin tabbatar da adalci, ƙarfafa hukumomi da kuma inganta tsarin mulkin dimokuraɗiyya a Nijeriya.














Discussion about this post