Kasar Sin ta bayyana adawa da duk wata musaya a hukumanci tsakanin Amurka da yankin Taiwan, haka kuma tana adawa da Amurkar ta sayar wa yankin Taiwan makamai.
Kakakain ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun ne ya bayyana haka a yau Alhamsi, inda ya bukaci Amurka ta aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin Sin da Amurkar suka cimma, ta girmama alkawura da yarjejeniyoyi, kuma ta tafiyar da batun Taiwan bisa taka tsantsan da hangen nesa.
Guo Jiakun ya kuma yi kira ga Amurka ta daina aikewa da mummunan sako ga ‘yan awaren Taiwan, kuma ta dauki kwararan matakai na kare zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Taiwan da kuma raya dangantakar Sin da Amurka cikin kwanciyar hankali. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post