Jam’iyyar APC a jihar Kebbi ta tabbatar da gwamna Nasir Idris a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a zaben shekarar 2027.
An tabbatar da hakan ne yayin zaben fidda gwani na gwamna da APC ta gudanar a filin wasa na Haliru Abdu da ke Birnin Kebbi ranar Alhamis, inda wakilai da mambobin jam’iyyar daga sassan jihar suka halarta.
Shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na APC kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Abdulmalik Mahmud, ne ya sanar da tabbatar da Idris a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.
Mahmud ya ce kwamitin ya je jihar Kebbi ne domin gudanar da zaɓen fidda gwanin tare da tabbatar da zaɓin da mambobin jam’iyyar suka yi.
Da yake jawabi bayan tabbatar da shi, gwamna Idris ya amince da takarar tare da yin alkawarin ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaban al’umma a faɗin jihar idan aka sake zaɓensa a shekarar 2027.
Haka kuma ya gode wa shugabannin jam’iyyar da tsoffin gwamnoni a jihar bisa goyon baya da kuma halartar da suka yi a yayin gudanar da zaɓen.















Discussion about this post