Da safiyar yau Laraba ne ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da takardar bayani mai taken “Kafa tsarin jagorancin harkokin duniya mai karin adalci: Akidun kasar Sin da shawararta da kuma matakanta”.
Takardar ta yi cikakken bayani a kan shawarar inganta tsarin jagorancin harkokin duniya da kasar Sin ta gabatar, musamman ta fannin kimiyya, da kuma ma’anarta ga duniya a wannan zamani da muke ciki, tare da bayyana matakan da kasar Sin ta dauka, da kuma nasarorin da ta cimma wajen sa hannu a inganta tsarin jagorancin harkokin duniya. Har ila yau, takardar ta yi kira ga sassan kasa da kasa da su aiwatar da shawarar inganta tsarin jagorancin harkokin duniya, don kafa tsari mai karin adalci.
A gun taron manema labarai da aka shirya dangane da takardar, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, wanda kuma shi ne ministan harkokin wajen kasar, Mr. Wang Yi, ya amsa tambayar da aka yi masa dangane da yadda ake komawa cikin yanayin yadda masu karfi ke cin zalin marasa karfi, tare da raunata karfin fada a ji na MDD, inda ya bayyana matsayin kasar Sin na kiyaye cudanyar bangarori daban daban, da goyon bayan rawar da MDD ke takawa. Wang Yi ya ce, ba wai MDD ba ta da muhimmanci ba ne, sai dai ba a mutunta da kiyaye ta yadda ya kamata.
A matsayinta na kasa ta farko da ta sanya hannu kan kundin tsarin dokokin MDD, kasar Sin tana son kiyaye karfin fada a ji na MDD ta hanyar aiwatar da shawarar inganta jagorancin harkokin duniya, kuma tana son hada kai da sassan kasa da kasa, a kokarin farfado da MDD da kuma kara bunkasa ta.
A yayin taron, Wang Yi ya yi bayani game da fannoni guda 4 da kasar Sin za ta dukufa domin inganta tsarin jagorancin harkokin duniya.
Da farko, ya ce za a farfado da ra’ayin raya yankuna gaba daya cikin hadin gwiwa. A bana, kasar Sin za ta gudanar da taron ganawar shugabannin kungiyar hadin gwiwar tattalin arzikin yankin Asiya da Pacifik ta APEC, inda za a samar da sabbin damammaki ga bunkasuwar kasashen dake yankin Asiya da Pacifik, har ma da kasashen duniya baki daya. Na biyu kuma, za a karfafa aikin gudanar da sabbin ayyuka. Na uku kuma, za a inganta aikin gina dandalolin jagorancin harkokin duniya. Kasar Sin ta yi maraba da sassan kasa da kasa, da su shiga kotun shiga tsakani ta kasa da kasa da kasar Sin ta yi kira a kafa, domin ba da gudummawa wajen warware sabanin dake tsakanin kasashen duniya cikin zaman lafiya. Na hudu kuma, ana sa ran kasashen duniya za su cimma matsayi daya kan tsarin jagorancin harkokin duniya.
A bana, kasar Sin za ta kira taron dandalin tattauna tsarin jagorancin harkokin duniya a sabon yankin Xiong’an karo na farko, inda za ta gayyaci wakilan bangarori daban daban daga kasashen duniya, domin tattauna yadda za a daidaita, da kuma kyautata tsarin jagorancin harkokin duniya.















Discussion about this post