Da safiyar yau Laraba ne ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin, ya kira taron manema labarai, inda ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasar Sin tana gaggauta aikin kafa kungiyar hadin gwiwar fasahar AI ta kasa da kasa, tana kuma maraba da halartar kasashen duniya, domin raya fasahar AI yadda ya kamata.
A watan Yulin bana, kasar Sin za ta kira babban taron fasahar AI na kasa da kasa na shekarar 2026, wato babban taron daidaita fasahar AI ta kasa da kasa a birnin Shanghai na kasar Sin.
Kasar Sin tana fatan bangarorin da abin ya shafa za su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu kan fasahar AI ta wannan dama. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post