• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Kasance Mai Hangen Nesa Da Samarwa Kanta Mafita A Duk Lokacin Da Ake Mata Zagon Kasa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Kasance Mai Hangen Nesa Da Samarwa Kanta Mafita A Duk Lokacin Da Ake Mata Zagon Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar gudanarwar kasar Sin ta fitar da sabbin matakan daukaka tattalin arzikin kasar da ma ingancin kayayyakin da aka kera a kasar.

A yanzu haka, kasar Sin ce babbar mai bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin duniya duk da kalubale da rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Don haka, kara karfafa tattalin arzikinta fiye da yadda yake a yanzu, zai bayar da gagarumar gudunmawa ga farfadowar tattalin arzikin duniya da ma kasashe masu tasowa.

  • An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

A cewar sanarwar da majalisar gudanarwar kasar Sin ta fitar jiya, zuwa shekarar 2025, za a bunkasa ingancin kayayyaki kirar kasar Sin. A yanzu haka, kayayyakin kasar Sin sun karade ko ina a fadin duniya, kusan babu gidan da za a shiga ba tare da ganin wani abu da kasar Sin ta kera ba, wannan yana nuna irin nasarar da Sin ta samu wajen kera kayayyaki masu inganci da kuma rahusa. A ganina, hauhawar farashin kayayyaki da aka samu a baya-bayan nan a kasashe masu tasowa har ma da manyan kasashe, na da nasaba da matakan yaki da annobar COVID-19. Amma bisa la’akari da sabbin matakan da Sin ta dauka, da kuma aka riga aka fara aiwatarwa a bana, ba makawa, za a samu sauki a fadin duniya, kuma kasashe masu tasowa za su samu damar amfana daga kayayyaki masu inganci da masana’antun kasar Sin za su samar.

Haka kuma sanarwar ta ce, kasar za ta inganta takarar masana’antu. A lokacin da ake kokarin dakile masana’antun kasar Sin ta kowacce fuska, wannan mataki zai kara karfafa musu gwiwa da kara samar musu da dimbin damarmaki a duniya, ta yadda babu wanda zai iya dakile su. Karfin takarar da za su yi da takwarorinsu na duniya, zai kara musu tagomashi da kasuwa da kuma samun karbuwa.

Hakika kasar Sin ta kasance mai hangen nesa a ko da yaushe, inda take samarwa kanta mafita a duk lokacin da ake kokarin dakile ta. Haka kuma ta kan mayar da hankali ne ainun wajen inganta kanta a cikin gida ba tare da kokarin dakile wani bangare ko yin zagon kasa ba. Shi ya sa har kullum take kara samun tagomashi da farin jini a duniya, abun da ya kamata sauran kasashe su nazarta domin su yi koyi da shi don tsayawa da kafarsu da samun ci gaba ba tare da dogaro da wani bangare ba.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauyin Kudi: Buhari Ya Gana Da Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Da Emefiele

Next Post

Sauyin Kudi: Bankin Zenith Ya Rufe Wasu Rassansa A Nijeriya Sakamakon Kai Masa Hari

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

3 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

4 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

5 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

6 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

7 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

17 hours ago
Next Post
Sauyin Kudi: Bankin Zenith Ya Rufe Wasu Rassansa A Nijeriya Sakamakon Kai Masa Hari

Sauyin Kudi: Bankin Zenith Ya Rufe Wasu Rassansa A Nijeriya Sakamakon Kai Masa Hari

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.