Kasar Sin ta mika kashi biyu na kayayyakin agaji ga gwamnatin kasar Lebanon, domin taimaka wa mutanen da yaki ya shafa.Agajin ya kunshi kayayyakin abinci na gaggawa da rumfuna da barguna da kayayyakin tsafta.
Yayin mika kayayyakin, jakadan Sin a Lebanon Chen Chuandong, ya bayyana cewa, manufar agajin da gwamnatin Sin ta bayar ita ce, taimakawa wajen saukaka wa mutanen Lebanon matsalar jin kai.
Ya ce, agajin na nuna dadaddiyar abotar da ke tsakanin kasashen biyu, yana cewa Sin na goyon bayan Lebanon ta kare ‘yanci da tsaro da hadin kai da kwanciyar hankalinta, haka kuma Sin din za ta ci gaba da bayar da agaji gwargwadon karfinta.
A nasu bangare, sakatare janar na kwamitin kula da ayyukan jin kai Bassam Naboulsi da kuma ministar kula da harkokin jama’a ta kasar Haneen Sayed, sun bayyana matukar godiya, suna cewa, agajin wanda ya zo a daidai lokacin da ake bukatarsa, ya nuna matsayin Sin na sahihiyar aminiyar Lebanon. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post