Tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya bayyana cewa addinin Musulunci na fuskantar matsalar ɓata suna a ƙarƙashin mulkin Bola Ahmed Tinubu.
Datti, ya yi wannan ikirari ne yayin da yake sukar yadda ake tafiyar da al’amuran ƙasa, yana mai cewa yadda ake tafiyar da gwamnati na iya shafar yadda ake kallon Musulunci a idon duniya.
Ya bayyana cewa wasu matakai da ke faruwa a ƙasar na haifar da damuwa, musamman dangane da yadda ake haɗa siyasa da addini, wanda a cewarsa zai iya janyo mummunan tasiri ga martabar Musulunci.
Wannan kalamai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan shugabanci, tsaro da kuma makomar siyasar Nijeriya gabanin zaɓen 2027.
Furucin Datti na nuna yadda wasu jiga-jigan siyasa ke kallon tasirin manufofin gwamnati ba kawai a fannin siyasa ba, har ma da tasirin su ga addini da kuma yadda ake kallon Nijeriya a idon duniya.















Discussion about this post