Shugaban ofishin kula da dokoki da ka’idoji na ma’aikatar kula da harkokin cinikayya ta kasar Sin ya bayyanawa ’yan jarida cewa, game da bukatun kafa tawagar masana kan matsalar dake tsakaninta da Sin da kungiyar EU ta gabatar ga hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO, kasar Sin za ta daidaita matsalar da tabbatar da hakkinta bisa tsarin daidaita matsaloli na hukumar WTO.
Kungiyar Tarayyar Turai EU ce, ta roki hukumar WTO ta kafa rukunin masana kan matsalar dake tsakaninta da Sin, wadda ke gaban WTO din.
Jami’in ya kara da cewa, kasar Sin ta jaddada sau da dama cewa, Sin tana dora muhimmanci kan tabbatar da ikon mallakar ilmi, da bin ka’idojin hukumar WTO da cika alkawarinta a hukumar, da kyautata dokokin tabbatar da ikon mallakar ilmi, kuma ana iya ganin nasarorin da Sin ta samu a wannan fanni. Ya ce kasar Sin ba ta ji dadin kudurin da EU ta tsara kan batun ba. (Zainab Zhang)














Discussion about this post