LMataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi kira ga kasashen duniya su yi kokarin taimaka wa kasashen yankin tsakiyar Afrika, ta yadda za su karfafa tsaronsu.
Sun Lei ya shaida wa Kwamitin Sulhu na MDD a jiya cewa, batutuwan tsaro a yankin tsakiyar Afrika na ci gaba da zama abun damuwa, yayin da ake samun tsanantar yanayin a kai a kai a yankin tafkin Chadi da kuma yawaitar hare-haren ta’addanci.
Ya ce ya kamata kasa da kasa su daukaka ra’ayin bai daya na hadin gwiwa da tsaro mai dorewa, da bayar da karin goyon baya ga bangarori kamar na wayar da kai game da yanayin da ake ciki da bayar da kudi da bayanan sirri da gargadin wuri, domin taimakawa kasashen dake yankin inganta karfinsu na tsaron kansu da kansu da karfafa matakan tsaro na yankin.
Haka kuma, ya kamata kasa da kasa su samar da cikakken goyon baya bisa yanayi na musamman na kasashen yankin a bangarori kamar na kudin gudanar da zabe da sulhu da shiga tsakani da aiwatar da gyare-gyare, ta yadda za su taka rawar gani wajen taimakawa wadannan kasashe samun kyautatuwar tsare tsarensu na siyasa da zaman lafiya.
Yayin taron G20 da ya gudana a watan da ya gabata, kasashen Sin da Afrika ta Kudu sun kaddamar da shawarar hadin gwiwa domin goyon bayan zamanantar da nahiyar Afrika. A cewar Sun Lei, a shirye Sin take ta hada hannu da kasashen Afrika wajen aiwatar da muhimman bangarorin hadin gwiwa da aka zayyana cikin shawarar da kuma taimakawa a bangarorin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba da wadata, a yankin tsakiyar Afrika. (FMM)














