Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a yau Talata cewa, kasar Sin ta nuna matukar bacin rai da kuma kakkausar suka kan yadda kasar Japan take da aniya mara kyau game da wurin bauta na Yasukuni.
Lin ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai na yau da kullum lokacin da aka nemi ya yi tsokaci kan ziyarar da ‘yan majalisar dokokin Japan suka kai fitaccen wurin bauta na Yasukuni da ke birnin Tokyo, wanda ya kasance wani tambari mai alamta amfani da karfin sojin Japan da kuma zaluncinta na lokacin yaki.
A lokacin da yake amsa wata tambaya mai alaka da ikirarin firaministar kasar Japan, Sanae Takaichi, na cewa ta shirya tsaf domin fuskantar “rikici na dogon lokaci” a yayin aikin wani kwamitin da aka dora wa alhakin nazarin manufofin kare kai da tsaron kasarta, Lin ya ce, ba wai kawai Japan ta gaza waiwaye tare da tsarkake ruhinta na yake-yaken zaluncin da ta yi a baya ba ne, har ma tana yunkuri ne na sake fadada amfani da karfin soji.
Don haka, dole ne dukkan kasashen duniya masu son zaman lafiya su kasance cikin taka-tsan-tsan tare da yin tsayin daka wajen nuna turjiya ga take-take na ganganci da Japan ke yi na kafa sabuwar akidar amfani da karfin soja. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














Discussion about this post