ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

by Muhammad
1 month ago

Majalisar Tarayya za ta ɗage zaman ta na majalisa a ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar halartar zaɓen fidda gwani na jam’iyyunsu gabanin babban zaɓen 2027.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana hakan ne a zaman majalisa na ranar Talata, inda ya ce ‘yan majalisa da dama ba za su samu halarta ba saboda shiga harkokin zaɓen fidda gwani.

Ya ce ɗage zaman na wucin gadi ya zama dole domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga harkokin siyasa a mazabunsu, duk da cewa kwamitocin majalisa za su ci gaba da gudanar da aikinsu a lokacin hutun.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Saboda haka, ‘yan majalisa da dama ba za su halarta ba. Don haka ya zama dole mu ɗage zaman na ɗan lokaci, amma kwamitoci za su ci gaba da ayyukan sa ido.”

Akpabio ya ƙara da cewa majalisar za ta kammala muhimman ayyukan dokoki kafin ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar komawa yankunansu domin zaɓen fidda gwani.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Muna son mu kammala sauran ayyuka kafin Alhamis, domin ‘yan majalisa su samu damar komawa ga jama’arsu su shiga zaɓen fidda gwani bisa tsarin jam’iyyunsu,” in ji shi.

Haka kuma ya roƙi shugabannin jam’iyyun siyasa da su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani yadda ba zai kawo cikas ga ayyukan majalisa ba.

“Ina kira ga shugabannin jam’iyyun siyasa su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani daga mako mai zuwa, domin a wannan makon muna zaman majalisa domin kammala ayyukanmu,” ya ƙara.

A Nijeriya, ɗage zaman majalisa domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga zaɓen fidda gwani ya zama ba sabon abu ba ne.

Ana gudanar da zaɓen fidda gwani ne bisa tanade-tanaden dokar zaɓe, kundin tsarin mulki da kuma ƙa’idojin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke fitarwa.

Dokar zaɓe ta tanadi hanyoyi uku na zaɓen fidda gwani, wato kai tsaye, a kaikaice, ko kuma ta hanyar yarjejeniya, muddin an bi ƙa’idojin dimokuraɗiyya.

Hukumar INEC na sa ido kan yadda ake gudanar da zaɓen fidda gwani, kuma rashin bin ƙa’ida na iya haifar da rikice-rikice ko hana ɗan takara tsayawa.

Bisa jadawalin INEC, ana sa ran jam’iyyun siyasa za su gudanar da zaɓen fidda gwani tsakanin 23 ga Afrilu zuwa 30 ga Mayu, 2027.

Jam’iyyar APC ta tsara nata zaɓen fidda gwani daga 15 zuwa 23 ga Mayu, yayin da tantance ‘yan takara zai gudana daga 6 zuwa 9 ga Mayu.

A ɓangaren jam’iyyar PDP mai alaƙa da Nyesom Wike, an tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranakun 17 da 18 ga Mayu, tare da sauran zaɓe daga baya.

Haka kuma wani ɓangaren Labour Party (LP) da Nenadi Usman ke jagoranta sun tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranar 23 ga Mayu.

INEC ta tsara zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a ranar 16 ga Janairu, 2027

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Ranar ’Yan Kwadago Ta Duniya Na Shekara Ta 2026 A Birnin Beijing

An Gudanar Da Bikin Ranar ’Yan Kwadago Ta Duniya Na Shekara Ta 2026 A Birnin Beijing

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.