ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

by Muhammad
3 months ago

Majalisar Tarayya za ta ɗage zaman ta na majalisa a ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar halartar zaɓen fidda gwani na jam’iyyunsu gabanin babban zaɓen 2027.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana hakan ne a zaman majalisa na ranar Talata, inda ya ce ‘yan majalisa da dama ba za su samu halarta ba saboda shiga harkokin zaɓen fidda gwani.

Ya ce ɗage zaman na wucin gadi ya zama dole domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga harkokin siyasa a mazabunsu, duk da cewa kwamitocin majalisa za su ci gaba da gudanar da aikinsu a lokacin hutun.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Saboda haka, ‘yan majalisa da dama ba za su halarta ba. Don haka ya zama dole mu ɗage zaman na ɗan lokaci, amma kwamitoci za su ci gaba da ayyukan sa ido.”

Akpabio ya ƙara da cewa majalisar za ta kammala muhimman ayyukan dokoki kafin ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar komawa yankunansu domin zaɓen fidda gwani.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

“Muna son mu kammala sauran ayyuka kafin Alhamis, domin ‘yan majalisa su samu damar komawa ga jama’arsu su shiga zaɓen fidda gwani bisa tsarin jam’iyyunsu,” in ji shi.

Haka kuma ya roƙi shugabannin jam’iyyun siyasa da su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani yadda ba zai kawo cikas ga ayyukan majalisa ba.

“Ina kira ga shugabannin jam’iyyun siyasa su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani daga mako mai zuwa, domin a wannan makon muna zaman majalisa domin kammala ayyukanmu,” ya ƙara.

A Nijeriya, ɗage zaman majalisa domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga zaɓen fidda gwani ya zama ba sabon abu ba ne.

Ana gudanar da zaɓen fidda gwani ne bisa tanade-tanaden dokar zaɓe, kundin tsarin mulki da kuma ƙa’idojin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke fitarwa.

Dokar zaɓe ta tanadi hanyoyi uku na zaɓen fidda gwani, wato kai tsaye, a kaikaice, ko kuma ta hanyar yarjejeniya, muddin an bi ƙa’idojin dimokuraɗiyya.

Hukumar INEC na sa ido kan yadda ake gudanar da zaɓen fidda gwani, kuma rashin bin ƙa’ida na iya haifar da rikice-rikice ko hana ɗan takara tsayawa.

Bisa jadawalin INEC, ana sa ran jam’iyyun siyasa za su gudanar da zaɓen fidda gwani tsakanin 23 ga Afrilu zuwa 30 ga Mayu, 2027.

Jam’iyyar APC ta tsara nata zaɓen fidda gwani daga 15 zuwa 23 ga Mayu, yayin da tantance ‘yan takara zai gudana daga 6 zuwa 9 ga Mayu.

A ɓangaren jam’iyyar PDP mai alaƙa da Nyesom Wike, an tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranakun 17 da 18 ga Mayu, tare da sauran zaɓe daga baya.

Haka kuma wani ɓangaren Labour Party (LP) da Nenadi Usman ke jagoranta sun tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranar 23 ga Mayu.

INEC ta tsara zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a ranar 16 ga Janairu, 2027

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
An Gudanar Da Bikin Ranar ’Yan Kwadago Ta Duniya Na Shekara Ta 2026 A Birnin Beijing

An Gudanar Da Bikin Ranar ’Yan Kwadago Ta Duniya Na Shekara Ta 2026 A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.