Majalisar Tarayya za ta ɗage zaman ta na majalisa a ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar halartar zaɓen fidda gwani na jam’iyyunsu gabanin babban zaɓen 2027.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana hakan ne a zaman majalisa na ranar Talata, inda ya ce ‘yan majalisa da dama ba za su samu halarta ba saboda shiga harkokin zaɓen fidda gwani.
Ya ce ɗage zaman na wucin gadi ya zama dole domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga harkokin siyasa a mazabunsu, duk da cewa kwamitocin majalisa za su ci gaba da gudanar da aikinsu a lokacin hutun.
Ya ce: “Saboda haka, ‘yan majalisa da dama ba za su halarta ba. Don haka ya zama dole mu ɗage zaman na ɗan lokaci, amma kwamitoci za su ci gaba da ayyukan sa ido.”
Akpabio ya ƙara da cewa majalisar za ta kammala muhimman ayyukan dokoki kafin ranar Alhamis domin bai wa ‘yan majalisa damar komawa yankunansu domin zaɓen fidda gwani.
“Muna son mu kammala sauran ayyuka kafin Alhamis, domin ‘yan majalisa su samu damar komawa ga jama’arsu su shiga zaɓen fidda gwani bisa tsarin jam’iyyunsu,” in ji shi.
Haka kuma ya roƙi shugabannin jam’iyyun siyasa da su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani yadda ba zai kawo cikas ga ayyukan majalisa ba.
“Ina kira ga shugabannin jam’iyyun siyasa su tsara jadawalin zaɓen fidda gwani daga mako mai zuwa, domin a wannan makon muna zaman majalisa domin kammala ayyukanmu,” ya ƙara.
A Nijeriya, ɗage zaman majalisa domin bai wa ‘yan majalisa damar shiga zaɓen fidda gwani ya zama ba sabon abu ba ne.
Ana gudanar da zaɓen fidda gwani ne bisa tanade-tanaden dokar zaɓe, kundin tsarin mulki da kuma ƙa’idojin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ke fitarwa.
Dokar zaɓe ta tanadi hanyoyi uku na zaɓen fidda gwani, wato kai tsaye, a kaikaice, ko kuma ta hanyar yarjejeniya, muddin an bi ƙa’idojin dimokuraɗiyya.
Hukumar INEC na sa ido kan yadda ake gudanar da zaɓen fidda gwani, kuma rashin bin ƙa’ida na iya haifar da rikice-rikice ko hana ɗan takara tsayawa.
Bisa jadawalin INEC, ana sa ran jam’iyyun siyasa za su gudanar da zaɓen fidda gwani tsakanin 23 ga Afrilu zuwa 30 ga Mayu, 2027.
Jam’iyyar APC ta tsara nata zaɓen fidda gwani daga 15 zuwa 23 ga Mayu, yayin da tantance ‘yan takara zai gudana daga 6 zuwa 9 ga Mayu.
A ɓangaren jam’iyyar PDP mai alaƙa da Nyesom Wike, an tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranakun 17 da 18 ga Mayu, tare da sauran zaɓe daga baya.
Haka kuma wani ɓangaren Labour Party (LP) da Nenadi Usman ke jagoranta sun tsara zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a ranar 23 ga Mayu.
INEC ta tsara zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a ranar 16 ga Janairu, 2027















Discussion about this post