A yau Laraba, memban ofishin siyasa a kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin, kana mataimakin firaministan kasar He Lifeng, ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da habaka bude sassan fannonin hada-hadar kudi cikin kwanciyar hankali, tare da maraba da cibiyoyin hada-hadar kudi daga dukkan kasashen duniya, don zurfafa kasancewarsu a kasuwar Sin, da kuma raba damarmmakin ci gaba na kasar.
He ya bayyana hakan ne a bikin bude taron dandalin tattaunawa na Lujiazui na shekarar 2026 a birnin Shanghai.
Ya ce Sin za ta bi hanyar samun ci gaban hada-hadar kudi mai salo irin nata, da ba da hidima ga ci gaban tattalin arziki mai inganci, da kuma ingiza kwanciyar hankali a tattalin arzikin duniya. (Safiyah Ma)















Discussion about this post