Kasar Sin ta shirya harba kumbon Shenzhou-23 mai dauke da ‘yan sama jannati da misalin karfe 11:08 na dare a gobe Lahadi, daga cibiyar harba taurarin dan Adam ta Jiuquan dake arewa maso yammacin kasar.
Hukumar kula da ayyukan sama jannati ta kasar Sin ce ta sanar da hakan yau Asabar, inda ta ce ‘yan sama jannati sun hada da Zhu Yangzhu da Zhang Zhiyuan da Lai Ka-ying, inda Zhu Yangzhu zai kasance shugaban tawagar. Kuma daya daga cikin ‘yan sama jannatin zai gudanar da aiki na tsawon shekara 1.
Ayyukan ‘yan sama jannati sun hada da binciken muhallin sararin samaniya da ayyuka a wajen cibiyar binciken samaniya ta Sin da jigilar kayayyaki da shirye-shiryen ilmantarwa da wayar da kan al’umma da sauransu.
Hukumar ta kuma sanar da cewa, an shirya harba na’urar binciken duniyar wata ta Sin ta Chang’e-7 a rabi na biyu na bana, kuma za ta gudanar da ayyukan nazarin muhalli da albarkatu a yankin kudancin duniyar watan da gudanar da ayyukan hadin gwiwa na kasa da kasa, baya ga tura na’urar binciken, kasar Sin na sa ran tura wata tawagar ‘yan sama jannati duniyar watan a shekarar 2030. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post