Kisan ƙare dangi da ƴan ta’adda ke yi a Arewacin Nijeriya tare da cin karensu ba babbaka ya zama silar tarwatsa ɗimbin al’umma daga garuruwan su a muhallan su domin tsira da rai a bisa ga yadda yankunan su suka zama lahira kusa.
Yadda mayaƙan Boko- Haram a Arewa- Maso- Gabas da ɓarayin daji a Arewa Maso- Yamma da Arewa ta -Tsakiya suke ƙunar bakin wake, ƙone garuruwa, garkuwa da mutane da hanawa manoma noma albarkatun gona ba tare da hukumomin da lamarin ya shafa sun kawo ƙarshen gawurtacciyar matsalar ba tuni miliyoyin jama’a suka zama ƴan gudun hijira a cikin ƙasar su.
A kasafin kuɗin shekarar 2026, Gwamnatin Tarayya ta ware tsabar zunzurutun kuɗi naira na gugar naira har tirliliyan 5 da bilyan 41 domin kawar da matsalar tsaro wadda a 2025 aka keɓe naira tirliyan 4 da bilyan 9, haka ma a 2024 an keɓe naira tirliyan 3 da bilyan 85 sai dai har yanzu al’ummar ƙasa na ƙorafin ba su ga canji a ƙasa ba.
Da yawan jama’a na nuna damuwa kan duk da maƙuddan kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro da ƙwarewar jami’an sojojin Nijeriya amma ƴan ta’adda sun rinjaye su ba tare da sun shawo kan matsalar ba ta yadda a yau hatta jami’an tsaro ba su tsira daga hannun ƴan ta’adda ba.
Nijeriya na fuskantar yawaitar ƴan gudun hijira ta yadda hukumomin jin ƙai ke gargaɗin cewa rikita- rikitar da ke ruruwa na ƙara bazuwa fiye da wuraren da aka saba fama, lamarin da ke jefa rayuwar miliyoyin mutane cikin haɗari.
A dalilin tarwatsa garuruwa, miliyoyin al’umma sun tarwatse sun warwastu a yankuna da dama a matsayin ƴan gudun hijira waɗanda wasu ke a ƙarƙashin cibiyoyin da gwamnati ta assasa da ke da rajista a yayin wasu ke a a wasu wuraren a zaman kan su a cikin ƙunchi.
Bayanai daga ofishin majalisar ɗinkin duniya da ke kula da ƴan gudun hijira ya bayyana cewar Nijeriya na da kusan mutane miliyan 3.5 zuwa 3.7 da suka rasa muhallansu a cikin a shekarar 2025–2026.
An tattara alƙaluma ne tare da haɗin guiwar ƙungiyar kula da ƴan gudun hijira ta duniya da hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) da kuma ofishin Kwamishinan kula da ƴan gudun hijira na majalisar ɗinkin duniya.
Bayanan sun nuna adadin mutane sama da miliyan uku da suka rasa muhallansu ya sanya Nijeriya a cikin jerin ƙasashen da ke da mafi yawan masu gudun hijira a nahiyar Afurka.
Alƙaluman ƙididdigar sun nuna Arewa- maso- Gabas na da kusan mutane miliyan 2.25 da ke gudun hijira waɗanda galibin su sun bar gidajen su a sakamon rikiciin Boko- Haram da suka kwashe tsayin shekaru suna cin karensu ba babbaka.
Haka ma yankin Arewa- maso- Yamma da ke fama da hare- haren ta’addancin ɓarayin daji da garkuwa da mutane ne ke da kaso na biyu da aƙalla kusan mutane 718,126, sai kuma Arewa ta Tsakiya da ke da adadin mutane 604,640 da suka ƙauracewa gidajensu domin tsira da rai.
Sai dai wasu rahotanni sun nuna cewar babu tabbacin samun sahihan alƙaluman ƙididdigar ƴan gudun hijira domin ƙididdigar na iya samun tangarɗa saboda ba dukkanin ƴan gudun hijira ne ke zaune a sansanonin da ke da rajista ba, haka ma su kan sauya matsugunni daga wannan zuwa wancan, akwai kuma bambancin hanyoyin ƙididdiga, haka ma sababbin hare- hare na iya canza alƙaluman ƙididdigar.
Hukumar kula da ƴan gudun hijira da ƴan ci rani a ƙarƙashin jagorancin Tijjani Aliyu Ahmed ita ce babbar hukuma a Nijeriya da ke kula da lamurran neman mafaka tare da sa ido daga hukumar hana shige da fice.
An kafa hukumar ne a shekarar 1989, a lokacin mulkin Shugaba Ibrahim Babangida, hasalima hukumar ta bayyana cewar an ƙirƙire ta ne domin “tabbatar da kare haƙƙin ƴan gudun hijira da masu neman mafaka tare da ba su tallafin da suke buƙata domin gudanar da ayuwa cikin tsaro da mutunci.”
‘Yan gudun hijira na fuskantar ɗimbin matsalolin da suka dabaibaye rayuwarsu suka hana masu walwala da jin daɗi a sansanonin gudun hijira daban- daban waɗanda suke fatar samun agaji da kulawar musamman gabanin fita daga ƙangin da suke ciki ta hanyar komawa gidajen su.
Cinkoson jama’a a sansanonin gudun hijira da rashin tsafta kan haddasa yaɗuwar cututtuka kamar kwalara da zazzabin cizon sauro tare da matsanancin rashin abinci mai gina jiki musamman ga ƙananan yara.
Tantin wucin- gadi a wasu sansanonin gudun hijira ko kaɗan ba su kare mabuƙatan daga tsananin yanayi ta yadda a lokacin sanyi suke fuskantar tsananin sanyi, yayin da a lokacin damina kuma ambaliya ke shafar su sosai. A yanzu haka mafi yawan sansanin gudun hijira babu ma maganar tanti ko wata kariyar da suke samu.
Bugu da ƙari mata da ƴan mata a sansanonin gudun hijira na fuskantar barazanar sacewa, fyaɗe da cin zarafi, har ma a wasu lokuta ba su da zaɓi face bayar da jikin su domin samun abinci, hakan ya tilastawa wasu da dama shiga bahaguwar hanyar karuwancii.
Baya ga wannan dubban ƙananan yara ba sa samun damar zuwa makaranta a sansanonin gudun hijira. A wasu sansanonin a kan samu wasu da ke zuwa suna sadaukar da lokacin su wajen karantar da yaran, sai dai galibi ba wani ƙwaƙƙwaran karatu suke samu ba.
Rufe sansanoni da gwamnati ke yi tare da tilasta mayar da ƴan gudun hijira ba tare da samar da ingantaccen matsuguni ko hanyoyin samun abin yi ba, kan ƙara jefa dubban mutane cikin ƙunchi da talauci, musamman waɗanda aka mayar zuwa wurare marasa tsaro.
Tsarin magudanan ruwa ta hanyar yin bayan gida a fili na haifar da barazana mai tsanani ga lafiyar jama’a, yayin da samun tsaftataccen ruwa da ingantattun hanyoyin kula da tsafta da muhalli ke ci- gaba da kasancewa babban ƙalubale a sansanonin.
Haka ma rashin wadataccen abinci babbar matsala ce mai zaman kan ta musamman ga al’ummomin da a baya suke dogaro da kan su ta hanyar noma amma a yanzu sun koma gaba ɗaya suna jiran tallafin abinci daga waje wanda kuma ba ya da tabbas.
Wata babbar matsalar da ƴan gudun hijira ke fuskanta shine yadda gwamnatoci ke kasa yin hoɓɓasar da ta kamata domin mayar da su garuruwan su ta hanyar samar masu ingantaccen tsaro da kuma gazawa wajen samar masu sabbin matsuguni.
A ƙoƙarin bayar da kulawa ga waɗannan matsalolin, Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da tsare-tsare da manufofi daban-daban domin taimakawa ƴan gudun hijira domin sauƙaƙawa rayuwarsu musamman a jihohin da ke fama da rikice-rikice.
Daga cikin shirye-shiryen akwai Tsarin Gaggawa na 2026–2028 wanda aka ƙaddamar tare da haɗin guiiwar Tarayyar Turai da ƙungiyar ƴan gudun hijira ta duniya domin samar da matsuguni, ruwa mai tsafta da tallafin jin ƙai ga ƴan gudan hijira.
Haka kuma, Gwamnatin Tarayya ta goyi bayan aiwatar da wasu manufofin kan ƴan gudun hijira tare da fara aiwatar da su a jihohin Katsina da Zamfara domin samar da hanyoyin inganta rayuwarsu, ba su muhalli, tallafin sana’oi domin su ci-gaba da rayuwa a cikin aminci.
Bugu da ƙari a wannan shekarar, gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shirin jin ƙai da magance talauci ta hanyar haɗa kai wajen yaƙi da talauci da taimakon gaggawa ga al’umma masu rauni ciki har da ƴan gudun hijira da ke warwatse a cikin al’umma.
A bisa ga yadda gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da manufofii da tsare- tsaren kula da ƴan gudun hijira a ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan hukumar kula da ƴan gudun hijira da ci- rani na ƙasa, Tijjani Aliyu Ahmed, ya bayyana cewar hakki ne da ya rataya a wuyan gwamnatin tarayya ta inganta rayuwar waɗanda matsalar ta shafa.
A ƙarkashin jagorancinsa, an fara aiwatar da tsare-tsare mayar da ƴan gudun hijira gida da kuma sake tsugunar da su tare da gina sabbin matsugunai, horas da sana’o’i da kuma inganta haɗin guiwar hukumomi.
Duk da haka LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar ƴan gudun hijira dama na kukan rashin kulawa yadda ya kamata daga gwamnati da hukumomin da lamarin ya shafa ta yadda galibi ba su da zaɓi face yawon bara domin samun abin da za su ci tare da kula da ƴaƴan su.
Gwamnatin Borno a ƙarkashin jagorancin Gwamna Babagana Umara Zulum na daga cikin waɗanda suka taka muhimmiyar rawa wajen kula da ƴan gudun hijira domin a cikin ƴan shekaru, gwamnatin ta mayar da hankali kan rufe sansanonin ƴan gudun hijira a Maiduguri tare da ƙarfafa musu guiwar komawa garuruwan su na asali.
Gwamna Zulum ya sha bayyana cewa zaman dogon lokaci a sansani ba abu ne mai ɗorewa ba don haka komawa gida shi ne mafita ta din-din-din. A kan wannan gwamnatin ta: gina gidajen da ta sake tsugunar da mutane a garuruwa kamar Bama, Ngala da Dikwa tare da gyara da sake gina makarantu, asibitoci da muhimman ababen more rayuwa da kuma
haɗa kai da jami’an tsaro domin inganta tsaro a yankunan da aka sake tsugunar da jama’a.
Gidauniyar ASSATAHIR ta yi fice wajen sanyayawa marasa galihu musamman marayu, mata da ƙananan yara, ta bayar da himma wajen bayar da gagarumar gudunmuwa wajen kawar da matsalolin ƴan gudun hijira da inganta jin daɗin su ta hanyar tallafa masu a lokacin da suka fi buƙatar agaji.
Gidauniyar ASSATAHIR wadda Malam Aliyu Sidi Attahir ya assasa kan ziyarci sansanonin gudun hijira da ke Sakkwato musamman a Ramen Kura da Guiwa Eka tare da jajanta masu kan halin da suke ciki tare da ba su tallafin musamman domin sauƙaƙawa halin da suke ciki.
Ɗaya daga cikin ƴan gudun hijira a Sakkwato, Abubakar Hassan ya bayyana cewar yadda Gidauniyar ASSATAHIR ke ƙoƙarin share masu hawaye da za a samu ire- iren ƙungiyoyi masu zaman kan su da za su riƙa bayar da kulawar musamman ga ƴan gudun hijira da matsalolin su sun zama tarihi.
A birnin tarayya, Idriss Ibrahim Halilu shine ke kula kuma kakakin sansanonin ƴan gudun hijira 18 da ke Abuja ya kuma bayyana cewa kusan kashi 98 cikin 100 na tallafin abinci da kayan more rayuwa da sansanonin gudun hijira ke samu na fitowa ne daga hannun mutane masu zaman kansu yana cewar rawar da gwamnati ke takawa a wannan fanni ƙalilan ce.
A ra’ayin wani ɗan gudun hijira a Zamfara, Haruna Magaji ya bayyana cewar “Mun jima muna rayuwa cikin wahala domin taimako daga gwamnati ba ya zuwa akai-akai kuma idan ya zo ma ba zai wadace mu ba. Yawancinmu muna dogaro ne da taimakon jama’a ko ƙungiyoyi masu zaman kansu. Don haka muna buƙatar gwamnati ta ƙara kulawa da mu musamman wajen abinci, lafiya da ilimi ga ƴaƴan mu.”















Discussion about this post