A yau Laraba, tawagogin Sin da Amurka sun gudanar da tattaunawa ta gaskiya, mai zurfi da kuma ma’ana a Koriya ta Kudu kan batutuwan tattalin arziki da kasuwanci da suka shafi bangarorin biyu, kana da duba yadda za a kara fadada hadin gwiwa a aikace.
Mataimakin firaministan Sin, He Lifeng, wanda har ila yau shi ne jagoran bangaren Sin a harkokin tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Amurka, tare da jagoran bangaren Amurka, sakataren baitulmalin kasar, Scott Bessent, sun gudanar da shawarwarin kan batutuwan.
A karkashin muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma, bangarorin biyu sun tsaya kan ka’idar girmama juna, da zaman lafiya mai dorewa, kana da hadin gwiwar cin moriyar juna.
Kazalika, duk dai a yau din, shugaban Koriya ta Kudu, Lee Jae Myung, ya gana da mataimakin firaministan Sin, He Lifeng, a ofishinsa na shugaban kasa da ke birnin Seoul. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














Discussion about this post