ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kawancen Sin Da Rasha Na Kara Tabbatar Da Amincincewa Da Junansu A Duniya

by Sulaiman
3 weeks ago

Dangantaka tsakanin Sin da Rasha na ci gaba da kara karfi a matsayin daya daga cikin manyan hadin gwiwar siyasa da tattalin arziki a duniya. Tsawon shekaru, kasashen biyu sun gina alaka mai dorewa bisa amincewa da juna, hadin gwiwar makamashi, kasuwanci, tsaro, da kuma goyon bayan juna a manyan batutuwan duniya. Wannan kusanci ya sa Beijing da Moscow ke zama abokan hulda da ke neman tabbatar da zaman lafiya da daidaito a tsarin duniya wanda a yanzu haka yake fuskantar sauye-sauye da ba a taba ganin irinsu ba a karni guda da ya gabata.

Bayan shugaba Xi ya tarbi shugaba Putin da bikin maraba na musamman a wajen zauren al’umma da ke tsakiyar Beijing, shugabannin biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi bunkasa kasuwanci, makamashi, fasaha, da hadin gwiwar diflomasiyya.

Masana harkokin siyasa na ganin cewa wannan ziyara wata alama ce ta kudurin kasashen biyu na kara zurfafa alakarsu musamman a wannan sabon zamani da ake fama da sauye-sauyen siyasa da tattalin arziki a duniya.Ziyarar ta kuma zo ce a daidai lokacin da ake gudanar da bikin baje kolin kayayyaki kirar Sin da Rasha karo na 10, inda ’yan kasuwar kamfanonin kasashen biyu ke yaukaka mu’amala a tsakaninsu.

ADVERTISEMENT

Bikin baje kolin wanda aka fara gudanarwa a shekarar 2014, a bana yana gudana ne a birnin Harbin na Sin, inda yake samun halartar kamfanoni sama da 1500 daga kasashe da yankuna 46 na duniya.

Har ila yau, Sin da Rasha na ci gaba da hada kai wajen karfafa tsarin duniya mai bai wa kowace kasa damar yin tasiri ba tare da mamaya ko kashin dankali daga wata kasa guda ba. Hadin gwiwarsu a fannoni kamar na makamashi, binciken kimiyya, da musayar al’adu na nuna yadda suke kokarin samar da hadin kai mai dorewa. Haka nan, yawaitar ganawa tsakanin Xi Jinping da Vladimir Putin a matsayin shugabannin manyan kasashen biyu na duniya, na kara tabbatar da amincewa da juna a tsakanin kasashensu tare da karfafa dangantakar al’ummomin kasashen biyu.Kasar Sin dai na kara zama cibiyar da ke jan hankalin duniya saboda saurin bunkasar tattalin arzikinta da ci gaban fasaha da kuma gudunmawar da take bayarwa ga raya kasuwancin duniya, da kirkire-kirkire, da kuma shiga a dama da ita tare da sauke nauyin da ke wuyanta a matsayin babbar kasa a duniya ta hanyar gabatar da muhimman shawarwari na warware cukurkudaddun al’amuran duniya a fannin tsaro, inganta shugabanci, bunkasa wayewar kan bil’adama har ma da shiga gaba wajen samar da kyakkyawar makoma ta bai-daya ga dukkannin bil’adama. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing
  • Sulaiman
    Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

MASU ALAKA

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Next Post
Lai Ching-te Na Shan Suka Yayin Da Yunkurin Neman ’Yancin Taiwan Ke Rasa Goyon Baya

Lai Ching-te Na Shan Suka Yayin Da Yunkurin Neman ’Yancin Taiwan Ke Rasa Goyon Baya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

Shugaban Sin Na Jagorantar Bunkasa Dangantakar Sin Da Koriya Ta Arewa A Sabon Zamani

June 11, 2026
Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

Nijeriya da Habasha Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dawo Da Fursunonin Nijeriya Sama da 100

June 11, 2026
Za A Kammala Aikin Bututun Iskar Gas Na AKK A Disambar 2024 – NNPC

Na Yi Matuƙar Mamakin Sammaci A Kaina – Mele Kyari

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.