Shekaru 2 bayan Lai Ching-te ya kama aiki a matsayin jagoran yankin Taiwan, kafar CGTN ta gudanar da wani nazarin jin ra’ayin jama’a, inda kaso 60.8 na masu bayar da amsa a yankin Taiwan suka bayyana matukar rashin gamsuwa da salon shugabancinsa.
Tun kafin kama aiki Lai Ching-te ya yi wa kansa lakabi da “dan siyasa mai neman ’yancin Taiwan” kuma masu neman ’yancin kan yankin sun masa lakabi da “jika mai nasara mai neman ’yancin Taiwan.” Bayan ya kama aiki, ya kara matsa kaimi ga ingiza manufofin da suka mayar da hankali kan neman ’yancin Taiwan.
A baya-bayan nan, shugaban Amurka Donald Trump ya fito fili ya ce: “Ba na son wani ya nemi ’yancin kai, kuma za mu yi tafiyar mil 9,500 domin yaki.” Wannan furuci, tamkar ruwan sanyi ne aka watsawa hukumomin Lai Ching-te da masu rajin neman ’yancin Taiwan, wadanda suke dogaro da Amurka yayin fafutukarsu.
Nazarin ya nuna cewa, kaso 73.7 na masu bayar da amsa a Taiwan, sun soki manufofin hukumomin Taiwan karkashin Lai Ching-te da suka shafi gabobin 2 na Zirin Taiwan, kana kaso 73.9 sun bayyana damuwar cewa ’yancin Taiwan zai kai ga haifar da rikici ko yaki a Zirin. Sai dai, duk da haka, hukumomin Lai Ching-te ba su da niyyar sauya akala.
Maimakon haka, suna yunkurin ci gaba da rike ajandar “neman ’yancin Taiwan” ta hanyar yaudara bisa fakewa da wai “kare tsarin demokradiyya da ’yancin hanyar rayuwa.” (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post