Da safiyar yau, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai, inda ya gabatar da yanayin ci gaban masana’antu da fasahar sadarwa a rubu’in farko na shekarar nan ta 2026.
Yayin taron, wani jami’in ofishin ya yi karin haske game da yanayin da ake ciki dangane da gina manyan kayayyakin aikin sadarwa, da bayanai na kasar Sin, inda ya ce da farko karfin hanyar sadarwa ya samu ci gaba.
Ya ce ya zuwa karshen watan Maris, jimillar manyan tashoshin sadarwa na 5G a fadin kasar ya kai miliyan 4.958. Na biyu, hanyar sadarwa ta kara fadi.
Inda ya zuwa yanzu, kashi 100% na kauyuka a fadin kasar sun samu yanar gizo, kuma sama da kashi 95% sun samu hanyar sadarwa ta 5G. Na uku, ana amfani da hanyar sadarwa yadda ya kamata.
Ya zuwa yanzu, fasahar 5G da yanar gizo mai karfin gigabit sun shiga cikin manyan nau’ikan tattalin arziki 91 daga cikin 97.
Bugu da kari, a rubu’in farko na wannan shekara, wato daga watan Janairu zuwa Maris, karin darajar masana’antu masu girma a kasar Sin ta daga da kashi 6.1% bisa na makamancin lokaci na shekarar da ta gabata, kuma dukkan larduna 31 na babban yankin kasar sun samu karuwa mai kyau. Kazalika, gudunmawar masana’antu ga ci gaban tattalin arziki ta kai kusan kashi 40%. (Amina Xu)















Discussion about this post