ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Tasirin Amerika A Idon Duniya Ke Ci Gaba Da Dushewa

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
The White House is seen shortly before a storm May 30, 2025. (Francis Chung/POLITICO via AP Images)

The White House is seen shortly before a storm May 30, 2025. (Francis Chung/POLITICO via AP Images)

Ga dukkan alamu al’amuran siyasa da na shugabanci a duniya suna daukar wani sabon salo, musamman kan lamuran duniya.

Kowa dai ya san da cewa Amerika ta dade tana yin kaka gida a cikin harkokin duniya, musamman a fannin siyasa da tattalin arziki, wato sai abin da take so za a yi, domin ita ce ke juya akalar tattalin arzikin duniya, ta sanya takunkumin karya tattalin arziki ga duk kasar da ta bijirewa manufofinta, ko kuma ta tumbuke shugaban kasar da ya ki amincewa ya zama dan amshin shatan Amerika, ya Allah ko kai tsaye ko kuma irin abin da ya faru da shugaban kasar Venezuela.

Hakika zalunci ba ya dorewa, domin kuwa alamu suna bayyana cewa, wannan shugabanci na kama karya da Amerika ke aiwatarwa, ya fara samun koma baya. Kasashen duniya sun fara dawowa daga rakiyar shugabanci irin na zalunci.

ADVERTISEMENT

Hatta kawaye da ’yan koren Amerika sun fara juyawa Amerika baya a kan manufofinta na rashin adalci. Kamar kungiyar NATO ta ki amincewa ta shiga cikin yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da kasar Iran, shi ma firaministan Burtaniya ya fito karara ya ce Burtaniya ba za ta shiga cikin wannan yaki na rashin hankali ba.Yanzu haka dai kasar Sin ta zarce Amerika ta fannin samun goyon baya na jagoranci a duniya. Wannan ya bayyana ne a samakon wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da aka gudanar a shekara ta 2025, inda Sin ta samu kashi 36, yayin da Amerika ta samu kashi 31.

Da ma dai kasar ta Sin ta taba zarce Amerika a irin wannan kuri’ar jin ra’ayin jama’a kan shugabanci har sau biyu, wato lokacin gwamnatin Geoge W. Bush da kuma lokacin shugabancin Donald Trump a karo na farko.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Manyan abubuwan da suka haifar da wannan sauyi sun hada da yadda Sin take maida hankali kan sakamako mai kawo ci gaba a kasashe musamman masu tasowa. Akwai kuma batun hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashe wanda aka gina kan tubalin cude ni in cude ka.

Sannan sai batun sabunta manufar nan ta mutuntawa da kiyaye cikakken ’yancin kasa ba tare da la’akari da girma ko kankanta ba, ko kuma karfi ko rauni ba.

Wadannan batutuwa sun taimaka wajen baiwa Sin damar yin zarra da kwarjini a tsakanin kasashen duniya. Yayin da a waje daya ita kuma Amerika take ta fuskantar kalubale kan manufofinta na rashin adalci, zalunci da kuma rashin sanin ya kamata.Wani muhimmin abin da ya kara zubar da mutuncin Amerika shi ne yadda kasar ta fice daga kungiyoyi na kasa da kasa kimanin 66, wadanda suke ba da gudummuwa ta fannoni daban daban ga bil adam. Janye tallafin da Amerika ke baiwa irin wadannan kungiyoyi na kasa da kasa ya haifar da mummunan tasiri musamman ga kasashe masu tasowa.

A waje daya kuwa, sabanin hakan, kasar Sin ta kara bunkasa manufarta ta hadin gwiwa domin amfanin kowa da kowa.

Kasashe da dama suna amfana da Sin a fannoni daban daban, kamar tashoshin jiragen ruwa, filayen saukar jiragen sama, titunan mota, layukan dogo da sauransu. Kasashe da dama daga nahiyar Afirka, Asiya da Latin Amerika sun amfana da irin wannan manufa ta kasar Sin.

Kuma abin ban sha’awa a nan shi ne kasar Sin ba ta shimfida wasu sharudda ga kasa kafin samar da irin wadannan ababen more jin dadin rayuwa. Sannan kuma ta tsaya kan manufar nan ta kaucewa tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasashe. (Lawal Mamuda)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya

An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.