ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Tasirin Amerika A Idon Duniya Ke Ci Gaba Da Dushewa

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
The White House is seen shortly before a storm May 30, 2025. (Francis Chung/POLITICO via AP Images)

The White House is seen shortly before a storm May 30, 2025. (Francis Chung/POLITICO via AP Images)

Ga dukkan alamu al’amuran siyasa da na shugabanci a duniya suna daukar wani sabon salo, musamman kan lamuran duniya.

Kowa dai ya san da cewa Amerika ta dade tana yin kaka gida a cikin harkokin duniya, musamman a fannin siyasa da tattalin arziki, wato sai abin da take so za a yi, domin ita ce ke juya akalar tattalin arzikin duniya, ta sanya takunkumin karya tattalin arziki ga duk kasar da ta bijirewa manufofinta, ko kuma ta tumbuke shugaban kasar da ya ki amincewa ya zama dan amshin shatan Amerika, ya Allah ko kai tsaye ko kuma irin abin da ya faru da shugaban kasar Venezuela.

Hakika zalunci ba ya dorewa, domin kuwa alamu suna bayyana cewa, wannan shugabanci na kama karya da Amerika ke aiwatarwa, ya fara samun koma baya. Kasashen duniya sun fara dawowa daga rakiyar shugabanci irin na zalunci.

ADVERTISEMENT

Hatta kawaye da ’yan koren Amerika sun fara juyawa Amerika baya a kan manufofinta na rashin adalci. Kamar kungiyar NATO ta ki amincewa ta shiga cikin yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da kasar Iran, shi ma firaministan Burtaniya ya fito karara ya ce Burtaniya ba za ta shiga cikin wannan yaki na rashin hankali ba.Yanzu haka dai kasar Sin ta zarce Amerika ta fannin samun goyon baya na jagoranci a duniya. Wannan ya bayyana ne a samakon wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da aka gudanar a shekara ta 2025, inda Sin ta samu kashi 36, yayin da Amerika ta samu kashi 31.

Da ma dai kasar ta Sin ta taba zarce Amerika a irin wannan kuri’ar jin ra’ayin jama’a kan shugabanci har sau biyu, wato lokacin gwamnatin Geoge W. Bush da kuma lokacin shugabancin Donald Trump a karo na farko.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Manyan abubuwan da suka haifar da wannan sauyi sun hada da yadda Sin take maida hankali kan sakamako mai kawo ci gaba a kasashe musamman masu tasowa. Akwai kuma batun hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashe wanda aka gina kan tubalin cude ni in cude ka.

Sannan sai batun sabunta manufar nan ta mutuntawa da kiyaye cikakken ’yancin kasa ba tare da la’akari da girma ko kankanta ba, ko kuma karfi ko rauni ba.

Wadannan batutuwa sun taimaka wajen baiwa Sin damar yin zarra da kwarjini a tsakanin kasashen duniya. Yayin da a waje daya ita kuma Amerika take ta fuskantar kalubale kan manufofinta na rashin adalci, zalunci da kuma rashin sanin ya kamata.Wani muhimmin abin da ya kara zubar da mutuncin Amerika shi ne yadda kasar ta fice daga kungiyoyi na kasa da kasa kimanin 66, wadanda suke ba da gudummuwa ta fannoni daban daban ga bil adam. Janye tallafin da Amerika ke baiwa irin wadannan kungiyoyi na kasa da kasa ya haifar da mummunan tasiri musamman ga kasashe masu tasowa.

A waje daya kuwa, sabanin hakan, kasar Sin ta kara bunkasa manufarta ta hadin gwiwa domin amfanin kowa da kowa.

Kasashe da dama suna amfana da Sin a fannoni daban daban, kamar tashoshin jiragen ruwa, filayen saukar jiragen sama, titunan mota, layukan dogo da sauransu. Kasashe da dama daga nahiyar Afirka, Asiya da Latin Amerika sun amfana da irin wannan manufa ta kasar Sin.

Kuma abin ban sha’awa a nan shi ne kasar Sin ba ta shimfida wasu sharudda ga kasa kafin samar da irin wadannan ababen more jin dadin rayuwa. Sannan kuma ta tsaya kan manufar nan ta kaucewa tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasashe. (Lawal Mamuda)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

MASU ALAKA

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Next Post
An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya

An Sake Samun Ɓullar Cutar Korona A Nijeriya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.