ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Za A Ga Sauyi Bayan Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

Tawagogin Sin da Amurka sun fara gudanar da tattaunawa a karo na 6, kan batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, jiya Lahadi a birnin a Paris na Faransa, a wani lokaci da harkokin cinikayya a duniya ke cikin yanayi na hargitse saboda matakan son kai da Amurka ke dauka.

Yayin da kasar Sin ke fadada bude kofarta da kara gyara manufofi ta yadda za ta samar da kyakkyawan muhallin kasuwanci da na ci gaba ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na kasashen waje, a daya bangaren, Amurka na ci gaba da bullo da matakan kariyar cinikayya.

A baya-bayan nan, an ji yadda Amurka ta sanar da kaddamar da bincike mai lamba 301 kan kasashe da yankuna 60, ciki har da kasar Sin, bisa hujjojin rashin daukar mataki kan “Tilasta Kwadago” da “Fitar da Kayayyaki Fiye da Kima”.

ADVERTISEMENT

Irin wadannan matakai da Amurka ke ci gaba da bullowa da su daya bayan daya, suna mayar da hannun agogo baya kan irin ci gaban da ake samu da kuma kara hargitsa tsarin cinikayya da haifar da rashin tabbas a duniya.

Abun da ya kamata ta yi la’akari da shi shi ne, yayin da take kokarin durkusarwa ko dakile abokan cinikayyarta, to tana kara durkusar da kamfanoninta na ci gida, kuma hakan ba zai kai ta ga cimma burinta ba. Misali, wani sakamakon bincike na babban bankin Amurka ya ce, masu sayayya da masu harkokin kasuwanci ne suka biya kaso 90 na haraje-harajen da Amurka ta kakkaba bara. Har ila yau, wani rahoto na cibiyar JP Morgan ya ruwaito cewa, masu matsakaitan kamfanoni a Amurka ne suka fi jin jiki sanadiyyar matakan haraji na kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Babban misali da ya yi hannun riga da Amurka shi ne manufofin kasar Sin. Tana kara bude kofa da saukaka matakan cinikayya ga baki, amma kuma wannan bai sa ta ragu da komai ba, sai ma karin ci gaba da tagomashi da take samu. Wasu alkaluma da hukumar kididdga ta Sin ta fitar yau Litinin sun nuna yadda harkokin tattalin arziki suka samu tagomashi a farkon bana tsakanin Junairu da Fabrairu, inda karuwar manyan masana’antun kasa ya kai kaso 6.3 bisa dari, ma’aunin samar da sana’ar bayar da hidima ya karu da kaso 5.2, yawan kayayyakin yau da kullum da aka sayar ya kai kudin Sin yuan biliyan 8607.9, karuwar kaso 2.8 bisa dari, dukkansu idan aka kwatanta da makamancin lokaci a bara.

Ya zama wajibi Amurka ta lura cewa, babu inda rikici zai kai ta. Ya kamata kamar yadda ake da kyakkyawan fata game da tattaunawar karo na 6, a ga sauyi daga gare ta bayan kammaluwarsa. Sauyi mai aminci da dorewa da bangarorin biyu za su kara cin gajiyarsa, har ma da sauran sassan duniya. (Fa’iza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Fashewar Bam Ta Girgiza Maiduguri, Ana Fargabar Mutane Sun Mutu

Fashewar Bam Ta Girgiza Maiduguri, Ana Fargabar Mutane Sun Mutu

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.