ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Za A Ga Sauyi Bayan Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka?

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Amurka

Tawagogin Sin da Amurka sun fara gudanar da tattaunawa a karo na 6, kan batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, jiya Lahadi a birnin a Paris na Faransa, a wani lokaci da harkokin cinikayya a duniya ke cikin yanayi na hargitse saboda matakan son kai da Amurka ke dauka.

Yayin da kasar Sin ke fadada bude kofarta da kara gyara manufofi ta yadda za ta samar da kyakkyawan muhallin kasuwanci da na ci gaba ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na kasashen waje, a daya bangaren, Amurka na ci gaba da bullo da matakan kariyar cinikayya.

A baya-bayan nan, an ji yadda Amurka ta sanar da kaddamar da bincike mai lamba 301 kan kasashe da yankuna 60, ciki har da kasar Sin, bisa hujjojin rashin daukar mataki kan “Tilasta Kwadago” da “Fitar da Kayayyaki Fiye da Kima”.

ADVERTISEMENT

Irin wadannan matakai da Amurka ke ci gaba da bullowa da su daya bayan daya, suna mayar da hannun agogo baya kan irin ci gaban da ake samu da kuma kara hargitsa tsarin cinikayya da haifar da rashin tabbas a duniya.

Abun da ya kamata ta yi la’akari da shi shi ne, yayin da take kokarin durkusarwa ko dakile abokan cinikayyarta, to tana kara durkusar da kamfanoninta na ci gida, kuma hakan ba zai kai ta ga cimma burinta ba. Misali, wani sakamakon bincike na babban bankin Amurka ya ce, masu sayayya da masu harkokin kasuwanci ne suka biya kaso 90 na haraje-harajen da Amurka ta kakkaba bara. Har ila yau, wani rahoto na cibiyar JP Morgan ya ruwaito cewa, masu matsakaitan kamfanoni a Amurka ne suka fi jin jiki sanadiyyar matakan haraji na kasar.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Babban misali da ya yi hannun riga da Amurka shi ne manufofin kasar Sin. Tana kara bude kofa da saukaka matakan cinikayya ga baki, amma kuma wannan bai sa ta ragu da komai ba, sai ma karin ci gaba da tagomashi da take samu. Wasu alkaluma da hukumar kididdga ta Sin ta fitar yau Litinin sun nuna yadda harkokin tattalin arziki suka samu tagomashi a farkon bana tsakanin Junairu da Fabrairu, inda karuwar manyan masana’antun kasa ya kai kaso 6.3 bisa dari, ma’aunin samar da sana’ar bayar da hidima ya karu da kaso 5.2, yawan kayayyakin yau da kullum da aka sayar ya kai kudin Sin yuan biliyan 8607.9, karuwar kaso 2.8 bisa dari, dukkansu idan aka kwatanta da makamancin lokaci a bara.

Ya zama wajibi Amurka ta lura cewa, babu inda rikici zai kai ta. Ya kamata kamar yadda ake da kyakkyawan fata game da tattaunawar karo na 6, a ga sauyi daga gare ta bayan kammaluwarsa. Sauyi mai aminci da dorewa da bangarorin biyu za su kara cin gajiyarsa, har ma da sauran sassan duniya. (Fa’iza Mustapha)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Fashewar Bam Ta Girgiza Maiduguri, Ana Fargabar Mutane Sun Mutu

Fashewar Bam Ta Girgiza Maiduguri, Ana Fargabar Mutane Sun Mutu

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.