Wata kotu a Landan ta wanke tsohuwar ministar man fetur ta Nijeriya, Diezani Alison-Madueke, daga dukkanin tuhume-tuhumen cin hanci guda shida.
Alƙalai a Kotun Southwark Crown sun ce ba ta da laifi bayan shari’ar da ta ɗauki lokaci mai tsawo, inda suka shafe sama da sa’o’i 46 suna yanke hukunci.
An zarge ta da karɓar cin hanci daga kamfanonin mai a lokacin da take minista tsakanin 2010 zuwa 2015, amma ta musanta dukkan zarge-zargen.
Lauyoyinta sun ce ba ta taɓa karɓar cin hanci ba, kuma ba ta da iko kai-tsaye kan rabon kwangiloli.
Sun kuma ce kuɗaɗen da aka yi amfani da su a shari’ar kuɗaɗen halal ne.
Kotun ta kuma wanke wasu mutane biyu da ake tuhuma, ciki har da wani jami’in harkar mai da kuma ɗan uwanta.
Lauyoyinta sun ce ta samu sassauci bayan shafe sama da shekaru 11 tana fuskantar bincike da shari’o’i, kuma yanzu za ta iya ci gaba da rayuwarta ta yau da kullum.
Har yanzu hukumomin Birtaniya ba su fitar da wata sanarwa kan hukuncin ba.















Discussion about this post