Dakarun Sojin Nijeriya sun ceto mutane biyar da aka yi garkuwa da su, bayan ‘yan ta’adda sun tsere sun bar su yayin wani farmaki da sojoji suka kai a Jihar Kogi.
A cikin wata sanarwa da rundunar sojoji ta 12 ta fitar, an bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 17 ga watan Yuni, 2026, yayin da ake ci gaba da yaƙi da ta’addanci a dazukan jihar.
Sojojin sun ce sun gudanar da haɗin gwiwar farmaki ta ƙasa da ta sama ne kan maɓoyar ‘yan ta’adda, inda suka gano mutanen da aka sace a hanyar Oshokoshoko zuwa Adankolo da ke cikin dajin Adankolo.
An gano waɗanda aka ceto ne bayan ruwan wuta da sojoji ke musu ya tilasta wa masu garkuwar tserewa daga sansanoninsu.
Daga nan ne sojoji suka tare su, suka fitar da su daga dajin, sannan suka kai su asibitin sojoji domin duba lafiyarsu.
Rundunar ta ƙara da cewa an yi wa mutanen tambayoyi domin tattara bayanan da za su taimaka wajen bin diddigin sauran ‘yan ta’adda a yankin.
Ana kuma shirin mayar da su wajen iyalansu bayan kammala binciken lafiya da harkokin gudanarwa.
Kwamandan rundunar ta 12, Birgediya Janar Kasim Umar Sidi, ya yaba wa sojojin bisa jarumta da ƙwarewa, yana mai cewa nasarar ta nuna ƙudirin sojoji na tabbatar da zaman lafiya a Kogi.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka wa yaƙi da garkuwa da mutane da sauran laifuka.














Discussion about this post