Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Belin El-Rufai Zuwa YuniBabbar Kotun Jihar Kaduna ta ɗage sauraron buƙatar beli na tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, zuwa makon farko na watan Yuni 2026.
A cewar rahoton ‘Channels Television’ a ranar Talata, Mai Shari’a Darius Khobo ya ɗage sauraron ne bayan ci gaba da shari’ar da ake yi, inda tsohon gwamnan ke fuskantar tuhume-tuhume da suka shafi zargin cin hanci da rashawa da kuma amfani da mukami ba ta hanyar da ta dace ba, wanda hukumar ICPC ta shigar.
Da yake magana bayan zaman kotun, lauyan tsohon gwamnan, Ukpon Akpan, ya soki yawan ɗage sauraron karar, yana mai bayyana hakan a matsayin “abin da ke da alaƙa da siyasa.”
Tsohon gwamnan ya halarci kotun a ranar Talata, inda ya isa da misalin ƙarfe 9 na safe cikin rakiyar jami’an ICPC da kuma DSS, yayin da hukumomin tsaro suka takaita zirga-zirga a harabar kotun.















Discussion about this post