Yau Talata, shugaban Sin Xi Jinping ya tattauna da takwaransa na Mozambique Daniel Francisco Chapo a birnin Beijing, wanda ke ziyarar aiki a Sin, kuma sun halarci bikin sanya hannu kan takardun hadin gwiwa tare.
Yayin ganawar, Xi ya bayyana cewa, tun da kasashen biyu suka kulla huldar diplomsiyya, Sin da Mozambique sun amince da juna kuma sun goyi bayan juna, wanda hakan ya zama abin koyi a fannin abokantakar Sin da Afirka da kuma hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa.
Ya ce kasashe masu tasowa, wadanda Sin da kasashen Afirka ke wakilta, sun kasance karfin tabbatar da adalci a cikin duniya mai cike da rudani da sauye-sauye.
Ya ce tasirin rikicin Gabas ta Tsakiya ya bazu zuwa kasashen Afirka, kuma Sin tana son hada hannu da kasashen Afirka don magance wadannan kalubale, tare da hada kai wajen inganta zaman lafiya da ci gaba.
A nasa bangare, Chapo ya bayyana cewa aiwatar da sakamakon taron kolin Beijing na dandalin tattanawar hadin gwiwar Sin da Afirka da kuma manufar soke harajin kwastam ga dukkan kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashen Afirka da suka kulla huldar diplomasiyya da Sin, sun samar da muhimmin tallafi ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasashen Afirka, kuma ya gode wa Sin da goyon bayan da take bayarwa.
Bugu da kari, shugabannin kasashen biyu sun amince da daukaka dangantakar kasashensu zuwa al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Mozambique a sabon zamani.
Haka kuma a yau din, shugaba Xi ya gana da mamban hukumar siyasa ta tsakiya ta jam’iyyar LPRP ta kasar Laos kuma mataimakin firaministan kasar, Saleumxay Kommasith, wanda ke ziyara a Sin a matsayin manzon musamman na babban sakataren kwamitin koli na jam’iyyar LPRP ta kasar Laos, kana shugaban kasar Thongloun Sisoulith. (Safiyah Ma)















Discussion about this post